< 1 Chroniques 20 >

1 Or il arriva qu’après le cours d’une année, au temps que les rois ont coutume d’aller à la guerre, Joab assembla l’armée, l’élite de la milice, et ravagea la terre des enfants d’Ammon; puis il alla et assiégea Rabba; mais David demeura à Jérusalem pendant que Joab battit Rabba et la détruisit.
Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
2 Or David enleva la couronne de la tête de Melchom, et il y trouva un talent d’or pesant et des pierreries très précieuses, et il s’en fit un diadème; il enleva aussi une grande quantité de dépouilles de la ville;
Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
3 Mais le peuple, qui y était, il l’en retira, et fit passer sur eux les traîneaux, les herses et les chars armés de fers; en sorte qu’ils fussent coupés en deux et broyés: ainsi fit David à toutes les villes des enfants d’Ammon, et il revint avec tout son peuple à Jérusalem.
ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
4 Après cela, on entreprit une guerre à Gazer contre les Philistins, en laquelle Sobochaï de Husathi tua Saphaï de la race des Raphaim, et il les humilia.
Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
5 On fit encore contre les Philistins une autre guerre, en laquelle Adéodat, fils de Saltus, Bethléhémite, tua le frère de Goliath, le Géthéen, dont le bois de la lance était comme une ensouple de tisserands.
Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
6 Mais, de plus, il arriva une autre guerre à Geth, en laquelle était un homme très grand, qui avait six doigts, c’est-à-dire, en tout vingt-quatre; qui lui-même aussi était sorti de la race de Rapha.
Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
7 Celui-ci blasphéma Israël; et Jonathan, fils de Samaa, frère de David, le tua. Ce sont là les enfants de Rapha, à Geth, lesquels tombèrent sous la main de David et de ses serviteurs.
Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
8
Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.

< 1 Chroniques 20 >