< Romains 5 >
1 Étant donc justifiés par la foi, nous avons la paix avec Dieu, par notre Seigneur Jésus-Christ,
Tun da shike mun sami barata, sabili da bangaskiya, mun sami salama tare da Allah ta wurin Yesu Almasihu.
2 qui nous a fait aussi avoir accès, par la foi, à cette grâce dans laquelle nous demeurons fermes; et nous nous glorifions dans l'espérance de la gloire de Dieu.
. Ta wurin sa kuma mun sami iso zuwa ga alheri inda muke tsayawa albarkacin bangaskiyarmu. Muna murna da gabagadin da Allah ya ba mu game da abin da zai faru, gabagadin da zamu dandana nan gaba cikin daukakar Allah.
3 Bien plus encore, nous nous glorifions même dans les afflictions, sachant que l'affliction produit la patience,
Ba kuwa haka kadai ba, amma muna murna da shan wahalolinmu. Mun san cewa shan wuya na haifar da
4 la patience la fidélité éprouvée, et la fidélité éprouvée, l'espérance.
Jimiri, Jimiri kuma na kawo amincewa, amincewa na kawo gabagadi game da abin da zai zo nan gaba.
5 Or, l'espérance ne rend pas confus, parce que l'amour de Dieu a été répandu dans nos coeurs par le Saint-Esprit, qui nous a été donné.
Wannan gabagadi wato begen da muke da shi baya kunyatarwa, domin kuwa an kwarara mana kaunar Allah a cikin zuciyarmu ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da aka ba mu.
6 En effet, lorsque nous étions encore sans force, Christ, au temps marqué, est mort pour des impies.
Domin kuwa ko yayin da muke raunana, Almasihu ya mutu a lokacin da ke dai dai domin marasa ibada.
7 Or, à peine voudrait-on mourir pour un juste; peut-être cependant, pour un homme de bien, quelqu'un se résoudrait-il à mourir.
To ai kuwa yana da wuya kwarai wani mutum ya yarda ya mutu don mutumin kirki ma. Watakila, wani na iyayin kasada ya yarda ya mutu don nagarin mutum.
8 Mais Dieu a fait éclater son amour envers nous en ce que, quand nous étions encore des pécheurs, Christ est mort pour nous.
Amma Allah ya tabbatar mana da kaunarsa a gare mu, don kuwa tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu domin mu.
9 Combien plus, étant maintenant justifiés par son sang, serons-nous sauvés par lui de la colère!
Balle ma yanzu, da muka barata ta wurin jininsa, za mu sami tsira daga fushin Allah.
10 Car si, lorsque nous étions les ennemis de Dieu, nous avons été réconciliés avec lui par la mort de son Fils, combien plus, étant réconciliés, serons-nous sauvés par sa vie!
Domin kuwa, in tun muna makiya, aka sulhunta mu da Allah ta wurin mutuwar Dansa, balle ma, yanzu da muka sami sulhu, zamu sami tsira ta wurin ransa.
11 Bien plus, nous nous glorifions en Dieu par notre Seigneur Jésus-Christ, par lequel nous avons maintenant obtenu la réconciliation.
Bama haka kadai ba, amma muna murna a cikin Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami wannan sulhu.
12 C'est pourquoi, comme, par un seul homme, le péché est entré dans le monde, et par le péché la mort, — et qu'ainsi la mort a passé sur tous les hommes, parce que tous ont péché.
Saboda haka, kamar yadda ta wurin mutum daya zunubi ya shigo cikin duniya, ta haka mutuwa ta shigo ta dalilin zunubi.
13 En effet, avant la loi, le péché était dans le monde; mais le péché n'est pas imputé, quand il n'y a point de loi.
Domin kuwa tun kafin a bada shari'a, zunubi na nan a duniya, amma ba' a lissafin zunubi in da ba shari'a.
14 Cependant la mort a régné, depuis Adam jusqu'à Moïse, même sur ceux qui n'avaient pas péché par une transgression semblable à celle d'Adam, lequel est l'image de Celui qui devait venir.
Duk da haka, mutuwa ta mallake tun daga Adamu har Musa, har ma wadanda basu yi zunubin keta umarni irin na Adamu ba, wanda yake misalin mai zuwan nan a gaba.
15 Mais il n'en est pas du don de la grâce comme de la faute. Car si, par la faute d'un seul, tous les autres sont morts, combien plus la grâce de Dieu et le don qu'il nous a fait, dans sa grâce, par un seul homme, Jésus-Christ, — ont-ils abondé pour tous les autres!
Amma kyautar ba kamar keta umarnin take ba. Domin in sabo da laifin mutum dayan nan ne, da yawa suke mutuwa, haka ma alherin sa da baiwarsa ta wurin mutum dayan nan, Yesu Almasihu, sai baiwar ta wadata zuwa ga masu yawa.
16 Et il n'en est pas de ce don comme des suites du péché commis par un seul homme: par suite d'une seule faute, le jugement a entraîné la condamnation; mais le don de la grâce, après un grand nombre de fautes, conduit à la justification.
Domin kyautar ba kamar sakamakon wannan da yayi zunubin bace. Ta haka din nan ne, hukuncin nan mai tsanani ya zo sabo da zunubin mutum dayan. Har yanzu dai, wannan baiwa ta yanci ta zo ne bayan laifuffuka masu yawa.
17 En effet, si, par la faute d'un seul, la mort a régné par ce seul homme, combien plus ceux qui reçoivent dans toute leur abondance la grâce et le don de la justice, régneront-ils dans la vie par un seul, Jésus-Christ!
Domin, idan sabo da laifin mutum dayan nan ne, mutuwa ta mallake, saboda dayan, haka ma wadanda suka karbi alheri mai yawa da kuma baiwar adalci ta wurin ran, Yesu Almasihu.
18 Ainsi donc, de même que, par une seule faute, la condamnation s'étend à tous les hommes, de même, par un seul acte de justice, la justification qui donne la vie s'étend aussi à tous.
Don haka, kamar yadda zunubin dayan ya sa hukunci ya zo kan dukka, haka ma aikin adalci na dayan zai kawo barata da rai ga mutane masu yawa.
19 Car de même que, par la désobéissance d'un seul homme, tous les autres ont été rendus pécheurs, ainsi, par l'obéissance d'un seul, tous les autres seront rendus justes.
Kuma kamar yadda rashin biyayyar dayan ta sa mutane masu yawan gaske su zama masu zunubi, haka ma ta biyayyar dayan mutane da yawan gaske za su sami adalci.
20 Or, la loi est intervenue, afin que la faute abondât; mais, où le péché a abondé, la grâce a surabondé,
Amma shari'a ta zo, inda ta sa zunubi ya habaka. Amma inda zunubi ya habaka, alheri ma ya habaka ribin ribi.
21 afin que, comme le péché a régné en donnant la mort, ainsi la grâce régnât par la justice, pour donner la vie éternelle par Jésus-Christ, notre Seigneur. (aiōnios )
Wannan ya faru ne, don kamar yadda zunubi yai mallaka zuwa mutuwa, haka kuma alheri ya mallaka zuwa adalci da rai na har abada ta wurin Yesu Almasihu Ubangijin mu. (aiōnios )