< Romains 1 >
1 Paul, serviteur de Jésus-Christ, appelé à être apôtre, mis à part pour annoncer l'Évangile de Dieu,
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 — Évangile que Dieu avait promis d'avance par ses prophètes dans les saintes Écritures,
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 et qui concerne son Fils né de la race de David, selon la chair,
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 et déclaré avec puissance Fils de Dieu, selon l'esprit de sainteté, par sa résurrection d'entre les morts, Jésus-Christ notre Seigneur,
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 par lequel nous avons reçu la grâce et l'apostolat, afin d'amener à l'obéissance de la foi, pour la gloire de son nom, toutes les nations,
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 dont vous faisiez partie, vous aussi, vous qui avez été appelés par Jésus-Christ. —
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 à tous les bien-aimés de Dieu qui sont à Rome, appelés à être saints. Que la grâce et la paix vous soient données de la part de Dieu, notre Père, et du Seigneur Jésus-Christ!
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 Avant tout, je rends grâces à mon Dieu, par Jésus-Christ, au sujet de vous tous, de ce que votre foi est renommée dans le monde entier.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 Car Dieu, que je sers en mon esprit, par la prédication de l'Évangile de son fils, m'est témoin que je fais sans cesse mention de vous
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 dans toutes mes prières, demandant de pouvoir enfin, par la volonté de Dieu, trouver une occasion favorable d'aller chez vous.
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 En effet, j'ai un ardent désir de vous voir, pour vous communiquer quelque don spirituel, afin que vous soyez affermis,
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 ou plutôt, afin que, me trouvant parmi vous, nous nous encouragions mutuellement par la foi qui nous est commune, à vous et à moi.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 Je ne veux pas, frères, vous laisser ignorer que j'ai souvent formé le projet d'aller vous voir, pour recueillir quelque fruit parmi vous comme parmi les autres nations; mais j'en ai été empêché jusqu'à présent.
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 Je me dois aux Grecs et aux Barbares, aux savants et aux ignorants.
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 Ainsi, autant qu'il dépend de moi, j'ai à coeur de vous annoncer l'Évangile, à vous aussi qui êtes à Rome.
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 En effet, je n'ai pas honte de l'Évangile, — parce qu'il est la puissance de Dieu pour le salut de tout croyant, du Juif premièrement, et aussi du Grec. —
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 Car, dans cet Évangile est révélée la justice de Dieu, qui s'obtient par la foi et qui conduit à la foi, ainsi qu'il est écrit: «Le juste vivra par la foi.»
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 La colère de Dieu, en effet, se révèle du ciel contre toute impiété et toute injustice des hommes, qui retiennent la vérité captive de l'injustice.
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 Car, ce que l'on peut connaître de Dieu est devenu manifeste pour eux. Dieu le leur ayant manifesté,
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 puisque ses perfections invisibles, sa puissance éternelle et sa divinité, se voient comme à l'oeil depuis la création du monde, quand on les considère dans ses ouvrages. Aussi sont-ils inexcusables, (aïdios )
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios )
21 parce que, tout en connaissant Dieu, ils ne lui ont pas donné la gloire qui appartient à Dieu, et ils ne lui ont pas rendu grâces; mais ils se sont égarés dans leurs vains raisonnements, et leur coeur sans intelligence a été rempli de ténèbres.
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 Se disant sages, ils sont devenus fous;
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 ils ont remplacé la gloire du Dieu incorruptible par des images qui représentent l'homme corruptible, des oiseaux, des quadrupèdes, des reptiles.
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 C'est pourquoi, Dieu les a livrés à l'impureté, suivant les convoitises de leurs coeurs, en sorte qu'ils déshonorent eux-mêmes leurs propres corps,
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 eux qui ont changé la vérité de Dieu en mensonge, et qui ont adoré et servi la créature au lieu du Créateur, lequel est béni éternellement. Amen! (aiōn )
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn )
26 C'est pour cela que Dieu les a livrés à des passions honteuses; car, parmi eux, les femmes ont changé l'usage naturel en un autre qui est contre nature.
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 De même aussi, les hommes, laissant l'usage naturel de la femme, se sont enflammés dans leurs désirs les uns pour les autres, commettant, homme avec homme, des infamies, et recevant en eux-mêmes le salaire dû à leur égarement.
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 Comme ils ne se sont pas souciés de conserver la connaissance de Dieu, Dieu les a livrés à un esprit pervers, de sorte qu'ils ont commis des actions indignes.
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 Ils sont remplis de toute espèce d'injustice, de perversité, de cupidité, de méchanceté; pleins d'envie, de meurtre, de dispute, de tromperie, de malignité;
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 délateurs, médisants, impies, insolents, arrogants, vaniteux, ingénieux à faire le mal, désobéissants envers leurs parents;
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 sans intelligence, sans loyauté, sans affection naturelle, sans pitié.
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 Et, bien qu'ils connaissent le décret de Dieu déclarant dignes de mort ceux qui commettent de telles actions, non seulement ils s'en rendent coupables, mais encore ils approuvent ceux qui les commettent.
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.