< Psaumes 119 >

1 Heureux ceux dont la conduite est intègre, Et qui suivent la loi de l'Éternel!
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Heureux ceux qui obéissent à ses enseignements, Qui le recherchent de tout leur coeur,
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Et qui ne commettent pas d'iniquité, Mais qui marchent dans les voies de l'Éternel!...
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu as donné tes commandements, ô Dieu, Pour qu'on les observe avec soin.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Daigne diriger ma conduite, Afin que j'observe tes préceptes!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Alors je n'aurai point à rougir, Quand je fixerai les regards sur tous tes commandements.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Je te célébrerai dans la droiture de mon coeur. Quand j'aurai appris tes justes jugements.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Je veux observer tes préceptes; Ne m'abandonne pas entièrement!
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Comment le jeune homme rendra-t-il pure sa conduite? C'est en restant fidèle à ta parole.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Je te cherche de tout mon coeur; Ne permets pas que je m'égare loin de tes commandements!
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 J'ai serré ta parole dans mon coeur. Afin de ne pas pécher contre toi.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Béni sois-tu, ô Éternel! Enseigne-moi tes préceptes.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 Mes lèvres énumèrent Tous les jugements que ta bouche a prononcés.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 Je trouve autant de joie à suivre tes enseignements, Qu'à posséder tous les trésors du monde.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Je méditerai tes commandements, Et je fixerai mes regards sur tes sentiers.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Je ferai mes délices de tes préceptes, Et je n'oublierai point tes paroles.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Accorde ce bienfait à ton serviteur: que je vive. Et que je garde ta parole!
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Dessille mes yeux. Afin que je contemple les merveilles de ta loi.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Je suis étranger sur la terre; Ne me cache pas tes commandements!
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Mon âme est consumée par l'amour Que lui inspirent tes lois, en tout temps.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu menaces les orgueilleux, Ces maudits qui s'écartent de tes commandements.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Éloigne de moi l'opprobre et le mépris; Car j'obéis à tes enseignements.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Les puissants eux-mêmes se sont assis, Et ils ont parlé contre moi; Mais ton serviteur médite tes préceptes.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Oui, tes enseignements font mes délices: Ils sont mes meilleurs conseillers.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Mon âme est abattue dans la poussière; Fais-moi revivre, selon ta parole!
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Je t'ai fait connaître ma conduite, et tu m'as approuvé; Enseigne-moi tes préceptes.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Montre-moi la voie que tu m'ordonnes de suivre. Et je méditerai tes merveilles.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Mon âme attristée se fond en larmes; Relève-moi, selon ta parole!
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Éloigne-moi de la voie du mensonge; Accorde-moi comme une grâce la connaissance de ta loi!
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 J'ai choisi la voie de la fidélité; J'ai mis tes jugements devant mes yeux.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Je me suis attaché à tes enseignements: Éternel, ne me rends pas confus!
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Je m'élancerai dans la voie de tes commandements, Quand tu auras mis mon coeur au large.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Éternel, apprends-moi à suivre tes préceptes, Et je les observerai jusqu'à la fin.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Donne-moi l'intelligence, et j'observerai ta loi: Je la pratiquerai de tout mon coeur.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Conduis-moi dans les sentiers de tes commandements; Car mon bonheur est de les suivre.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Incline mon coeur vers tes enseignements. Et non pas vers le gain.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Détourne mes yeux de la contemplation des choses vaines; Que je trouve la vie en marchant dans tes voies.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Accomplis envers ton serviteur ta promesse: Tu l’as donnée pour qu’on te craigne.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Détourne de moi l'opprobre que je redoute; Car tes jugements sont pleins de bonté.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 J'ai un ardent amour pour tes commandements! Fais-moi revivre par ta justice!
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Éternel, que tes bontés et ton salut Descendent sur moi, selon ta promesse!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Alors je saurai comment répondre à celui qui m'outrage; Car je me confie en ta parole.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Ne me refuse pas entièrement la faveur De rendre témoignage à la vérité; Car je mets mon attente en tes jugements.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Alors j'observerai ta loi constamment. Sans l'abandonner jamais.
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Je marcherai d'un pas libre; Car j'ai à coeur de suivre tes commandements.
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Je proclamerai tes volontés devant les rois. Et je n'en aurai aucune honte.
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Je ferai mes délices de tes commandements: Ils sont l'objet de mon amour.
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 J'élèverai mes mains vers tes commandements que j'aime. Et je méditerai tes préceptes.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Souviens-toi de la parole donnée à ton serviteur C'est sur elle que tu as fondé mon espérance.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 Ce qui me console dans mon affliction, C'est que ta parole me rend la vie.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Des orgueilleux me couvrent de railleries; Mais je ne m'écarte pas de ta loi.
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Je me rappelle tes jugements d'autrefois, ô Éternel, Et j'y trouve ma consolation.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 L'indignation me saisit, à cause des méchants Qui abandonnent ta loi.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Tes préceptes sont le sujet de mes cantiques, Dans la maison où j'habite en étranger.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 La nuit, je me rappelle ton nom, ô Éternel, Et j'observe ta loi.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Le bien qui m'est échu en partage. C'est de garder tes commandements.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Tu es ma part, ô Éternel. C'est pourquoi j'ai promis de garder tes paroles.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Je t'ai imploré de tout mon coeur: Aie pitié de moi, selon ta promesse!
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 J'ai fait l'examen de ma conduite, Et j'ai dirigé mes pas dans la voie de tes enseignements.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Je me hâte, je ne diffère point D'observer tes commandements.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Les pièges des méchants m'ont environné; Je n'ai point oublié ta loi.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Au milieu de la nuit, je me lève pour te célébrer, A cause de tes justes jugements.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Je suis le compagnon de tous ceux qui te craignent Et qui observent tes commandements.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 Éternel, la terre est pleine de ta bonté! Enseigne-moi tes préceptes.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Tu as fait du bien à ton serviteur, Éternel, selon ta parole.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Donne-moi un sens droit, ainsi que la vraie sagesse; Car j'ai foi en tes commandements.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Avant d'être affligé, je m'égarais; Mais, maintenant, j'observe ta parole.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu es bon, et tu manifestes ta bonté: Enseigne-moi tes préceptes.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Des orgueilleux ont ourdi contre moi des mensonges; Mais moi, j'obéis de tout mon coeur à tes ordres.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Leur coeur est épaissi comme de la graisse; Moi, je trouve mes délices dans ta loi.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Il m'est bon d'avoir été affligé: C'est ainsi que j'ai appris à connaître ta volonté.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 Les enseignements de ta bouche sont plus précieux pour moi Que des milliers de pièces d'or et d'argent.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Toi dont les mains m'ont formé et créé, Donne-moi l'intelligence, afin que je puisse apprendre tes lois.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Ceux qui te craignent me verront, et ils se réjouiront; Car j'espère en ta parole.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Je sais, ô Éternel, que tes jugements ne sont que justice: C'est dans ta fidélité que tu m'as affligé.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Que ta bonté soit donc ma consolation. Comme tu l'as promis à ton serviteur.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Que tes compassions s'étendent sur moi, et je vivrai; Car ta loi fait mes délices.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Que les orgueilleux soient confus. Eux qui m'oppriment sans motif; Et moi, je méditerai tes commandements.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Qu'ils reviennent à moi, ceux qui te craignent Et qui connaissent tes enseignements!
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Que mon coeur soit sincèrement attaché à tes préceptes, Afin que je n'aie pas à rougir de honte!
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Mon âme languit après son salut; J'espère en ta parole.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mes yeux se consument dans l'attente de ta promesse; Je dis: «Quand me consoleras-tu?»
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Je suis comme une outre dans un nuage de fumée; Mais je n'oublie pas tes préceptes.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Combien courte est la vie de ton serviteur! Quand donc feras-tu justice de ceux qui me persécutent?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Les orgueilleux ont creusé des pièges sous mes pas; Car jamais ils n'agissent selon ta loi.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Tous tes commandements témoignent de ta fidélité. Mes ennemis me persécutent sans motif; aide-moi!
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Encore un peu, et ils me faisaient disparaître de la terre! Mais je n'abandonne pas tes commandements.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Fais-moi revivre, toi qui es plein de bonté. Et j'obéirai aux enseignements de ta bouche.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Éternel, ta parole subsiste à jamais dans les cieux;
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Ta fidélité dure d'âge en âge! Tu as fondé la terre, et elle demeure ferme.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Tout subsiste aujourd'hui selon tes lois; Car toutes choses te servent.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Si ta loi n'eût fait mes délices. J'aurais déjà péri dans ma misère.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Jamais je n'oublierai tes commandements; Car c'est par eux que tu m'as fait revivre.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Je suis à toi, sauve-moi; Car je m'applique à suivre tes commandements.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Les méchants m'ont épié pour me faire périr; Mais je suis attentif à tes enseignements.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 J'ai vu des bornes à tout ce qui est parfait; Mais ta loi est d'une étendue sans fin.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 Combien j'aime ta loi! Tout le jour, je m'applique à la méditer.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Tes commandements me rendent plus sage Que mes ennemis, Parce qu'ils sont toujours présents à mon esprit.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 J'ai surpassé en sagesse tous ceux qui m'avaient instruit; Car tes enseignements sont l'objet de mes méditations.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 Je suis plus intelligent que les vieillards eux-mêmes; Car j'ai gardé tes commandements.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 J'ai détourné mes pas de tout mauvais chemin, Afin d'observer ta parole.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Je ne m'écarte point de tes lois, Parce que c'est toi qui m'as instruit.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Combien tes paroles sont douces à mon palais, Plus douces que le miel à ma bouche!
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Tes commandements m'instruisent; C'est pourquoi je hais tous les sentiers trompeurs.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Ta parole est un flambeau qui guide mes pas, Une lumière sur mon sentier.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 J'ai juré — et je tiendrai ma promesse. — D'observer tes justes lois.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Je suis extrêmement affligé: Éternel, fais-moi revivre, selon ta parole!
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Agrée les chants de louange Que t'offre ma bouche, ô Eternel, Et enseigne-moi tes commandements!
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Ma vie est continuellement en danger; Mais je n'oublie point ta loi.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Les méchants m'ont tendu des pièges; Mais je ne me suis pas écarté de tes commandements.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Tes enseignements sont pour toujours mon héritage; Ils sont la joie de mon coeur.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 J'ai rendu mon coeur docile à l'observation de tes préceptes, Pour toujours, jusqu'à la fin.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 Je hais les hommes au coeur double; Mais j'aime ta loi.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu es mon refuge et mon bouclier; J'espère en ta parole.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Retirez-vous de moi, méchants! Je veux garder les commandements de mon Dieu.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Soutiens-moi, selon ta promesse, Afin que je vive, Et ne me fais pas rougir d'avoir mis en toi mon espérance!
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Soutiens-moi: je serai sauvé. Et j'aurai toujours les yeux sur tes préceptes!
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu traites avec mépris tous ceux qui s'écartent de tes lois; Car toutes leurs machinations sont frappées d'impuissance.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tu rejettes, comme de l'écume. Tous les méchants de la terre. C'est pourquoi j'aime tes enseignements.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Ma chair tremble de frayeur en ta présence. Et je crains tes jugements.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 J'ai pratiqué ce qui est droit et juste; Ne m'abandonne pas à mes oppresseurs!
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Prends sous ta garde le bonheur de ton serviteur; Que les orgueilleux ne m'oppriment pas!
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mes yeux se consument dans l'attente de ton salut Et de tes promesses, ô Dieu juste.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Agis envers ton serviteur selon ta bonté, Et enseigne-moi tes préceptes.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Je suis ton serviteur; donne-moi l'intelligence, Afin que je puisse comprendre tes enseignements.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Le temps est venu d'agir en ta faveur, ô Éternel; Car on viole ta loi.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 C'est pourquoi j'aime tes commandements Plus que l'or, même que l'or fin.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 Ainsi je proclame que tous tes commandements sont droits, Et je hais tout sentier trompeur.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Tes enseignements sont admirables; Aussi mon âme les met-elle en pratique.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 Tes paroles sont une révélation qui éclaire; Elles donnent de l'intelligence aux simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 J'ouvre la bouche et je soupire; Car j'ai un grand amour pour tes commandements.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Regarde-moi et prends pitié de moi, Comme tu le fais pour ceux qui aiment ton nom.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Que ta parole affermisse mes pas. Et ne permets point que le péché domine sur moi.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Délivre-moi de l'oppression des hommes. Afin que j'observe tes commandements!
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Fais resplendir ta face sur ton serviteur, Et enseigne-moi tes préceptes!
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Des ruisseaux de larmes coulent de mes yeux. Parce que personne n'observe ta loi.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Tu es juste, ô Éternel, Et tes jugements sont droits.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tu prescris avec force, dans tes enseignements, La justice et la fidélité.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mon zèle me consume, Parce que mes ennemis ont oublié tes paroles.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Ta parole est parfaitement pure; Aussi est-elle chère à ton serviteur.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Je suis petit et méprisé; Mais je n'oublie pas tes commandements.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Ta justice est une justice éternelle, Et ta loi n'est que vérité.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 La détresse et l'angoisse m'ont atteint; Mais tes commandements font mes délices.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 Tes enseignements sont éternellement justes; Donne-m'en l'intelligence, afin que je vive!
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 Je t'invoque de tout mon coeur; réponds-moi, ô Éternel, Et je garderai tes préceptes.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Je crie vers toi; sauve-moi, Et je suivrai tes enseignements.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 Je devance l'aurore, et je t'invoque: Je mets mon espoir en ta parole.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mes yeux devancent les veilles de la nuit, Pour méditer ta promesse.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Dans ta bonté, ô Éternel, écoute ma voix; Dans ta justice, fais-moi revivre!
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Les voilà près de moi, ceux qui se précipitent dans le crime Et qui se détournent de ta loi.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Mais toi aussi, ô Éternel, tu t'approches de moi. Et tous tes commandements m'assurent de ta fidélité.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Depuis longtemps j'ai appris à connaître tes enseignements; Car tu les as établis pour toujours.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Regarde mon affliction, et délivre-moi; Car je n'ai pas oublié ta loi.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Défends ma cause, et délivre-moi; Fais-moi revivre, selon ta promesse!
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Le salut est loin des méchants. Parce qu'ils ne se soucient pas de tes préceptes.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Tes compassions sont en grand nombre, ô Éternel: Fais-moi revivre, suivant les arrêts de ta justice!
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Mes persécuteurs et mes adversaires sont nombreux; Mais je ne me détourne pas de tes enseignements.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 J'ai vu les infidèles, et j'en ai horreur: Ils n'observent pas ta parole.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Vois combien j'aime tes commandements; Éternel, fais-moi revivre, dans ta bonté!
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 Ta parole tout entière n'est que vérité, Et tous les arrêts de ta justice sont éternels.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Les grands m'ont persécuté sans motif; Mais mon coeur n'a craint que tes paroles.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 Je me réjouis de ta promesse. Comme celui qui a trouvé un grand trésor.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Je hais, j'ai en horreur le mensonge. Et j'aime ta loi.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Je te loue sept fois le jour. Pour les arrêts de ta justice.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Grande est la paix de ceux qui aiment ta loi: Rien ne peut les faire chanceler.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 Éternel, j'attends ta délivrance, Et je pratique tes commandements.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Mon âme obéit à tes enseignements, Et je les aime d'un grand amour.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 J'observe tes commandements et tes lois; Car toute ma conduite est présente à tes yeux.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Éternel, que mon cri parvienne jusqu'à toi! Donne-moi l'intelligence, conformément à ta parole!
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Que ma supplication s'élève jusqu'à toi! Délivre-moi, suivant ta promesse!
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Mes lèvres proclameront ta louange, Quand tu m'auras enseigné tes préceptes.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Ma langue célébrera ta parole; Car tous tes commandements sont justes.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Étends ta main pour me venir en aide; Car je veux obéir à tes commandements.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 Je soupire après ton salut, ô Éternel, Et ta loi fait mes délices.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Que mon âme vive, afin qu'elle te loue, Et que tes jugements soient mon appui!
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 Je suis errant comme une brebis perdue: Viens à la recherche de ton serviteur! Car je n'ai pas oublié tes commandements!
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.

< Psaumes 119 >