< Luc 24 >

1 Le premier jour de la semaine, de très grand matin, elles vinrent au tombeau, apportant les aromates qu'elles avaient préparés.
Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
2 Elles trouvèrent que la pierre avait été roulée loin de l'ouverture du tombeau;
Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
3 mais, étant entrées, elles ne trouvèrent point le corps du Seigneur Jésus.
Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
4 Elles ne savaient qu'en penser, lorsque deux hommes parurent devant elles, en vêtements brillants comme l'éclair.
Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
5 Et comme elles étaient saisies de frayeur et baissaient le visage vers la terre, ils leur dirent: Pourquoi cherchez-vous parmi les morts celui qui est vivant?
Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
6 Il n'est pas ici, mais il est ressuscité. Souvenez-vous de quelle manière il vous a parlé, lorsqu'il était encore en Galilée,
Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
7 et qu'il disait: Il faut que le Fils de l'homme soit livré entre les mains des pécheurs, qu'il soit crucifié et qu'il ressuscite le troisième jour.
cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
8 Alors elles se souvinrent des paroles de Jésus.
Sai matan suka tuna da kalmominsa,
9 Quand elles furent de retour du tombeau, elles annoncèrent toutes ces choses aux Onze et à tous les autres.
suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
10 C'étaient Marie-Madeleine, Jeanne, Marie, mère de Jacques; et les autres femmes, qui étaient avec elles, disaient les mêmes choses aux apôtres.
Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
11 Mais ces paroles leur firent l'effet d'une rêverie, et ils ne les crurent point.
Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
12 Cependant, Pierre se leva et courut au tombeau; et, s'étant baissé pour regarder, il ne vit que les linges qui étaient à terre; puis, il s'en alla chez lui, tout surpris de ce qui était arrivé.
Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
13 Ce même jour, deux des disciples allaient à un village, appelé Emmaüs, qui était à soixante stades de Jérusalem;
A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
14 et ils s'entretenaient de tout ce qui s'était passé.
Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
15 Or il arriva, comme ils s'entretenaient et discutaient ensemble, que Jésus lui-même s'approcha et se mit à marcher avec eux.
Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
16 Mais leurs yeux étaient privés du pouvoir de le reconnaître.
Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
17 Il leur dit: Quelles sont les paroles que vous échangez ainsi l'un avec l'autre, chemin faisant? Et ils s'arrêtèrent tout tristes.
Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
18 L'un d'eux, nommé Cléopas, lui répondit: Es-tu le seul étranger à Jérusalem, qui ne sache pas ce qui s'y est passé ces jours-ci?
Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
19 — Quoi donc? leur demanda-t-il. Ils lui répondirent: Ce qui est arrivé à Jésus de Nazareth, qui était un prophète puissant en oeuvres et en paroles, aux yeux de Dieu et de tout le peuple;
Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
20 comment les principaux sacrificateurs et nos magistrats l'ont livré pour être condamné à mort, et l'ont crucifié.
Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
21 Pour nous, nous espérions que ce serait lui qui délivrerait Israël; mais, avec tout cela, voici le troisième jour que ces choses sont arrivées.
Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
22 Il est vrai que quelques femmes, qui sont des nôtres, nous ont fort étonnés. Elles sont allées de grand matin au tombeau;
Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
23 puis, n'ayant pas trouvé son corps, elles sont venues nous dire que des anges leur sont apparus et leur ont déclaré qu'il était vivant.
Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
24 Quelques-uns des nôtres se sont aussi rendus au tombeau, et ils ont trouvé les choses comme les femmes l'avaient dit; mais lui, ils ne l'ont pas vu.
Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
25 Alors Jésus leur dit: gens sans intelligence et d'un coeur lent à croire tout ce qu'ont annoncé les prophètes!
Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
26 Ne fallait-il pas que le Christ souffrît ces choses pour qu'il entrât dans sa gloire?
Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
27 Puis, commençant par Moïse et continuant par tous les prophètes, il leur expliqua, dans toutes les Écritures, ce qui le concernait.
Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
28 Quand ils se trouvèrent près du village où ils se rendaient, Jésus semblait vouloir aller plus loin.
Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
29 Mais ils l'obligèrent à s'arrêter, en disant: Reste avec nous; car le soir approche, et le jour est déjà sur son déclin. Il entra donc pour rester avec eux.
Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
30 Comme il était à table avec eux, il prit le pain, et, après avoir rendu grâces, il le rompit et le leur donna.
Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
31 Alors leurs yeux s'ouvrirent, et ils le reconnurent; mais lui se déroba à leur vue.
Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
32 Et ils se dirent l'un à l'autre: Notre coeur ne brûlait-il pas au-dedans de nous, lorsqu'il nous parlait en chemin et nous expliquait les Écritures?
Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
33 Se levant à l'heure même, ils retournèrent à Jérusalem, et ils trouvèrent les Onze et d'autres disciples assemblés avec eux,
Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
34 qui leur dirent: Le Seigneur est vraiment ressuscité, et il est apparu à Simon.
cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
35 Eux, à leur tour, racontèrent ce qui leur était arrivé en chemin, et comment ils l'avaient reconnu lorsqu'il avait rompu le pain.
Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
36 Comme ils parlaient ainsi, Jésus lui-même se présenta au milieu d'eux et leur dit: La paix soit avec vous!
Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
37 Mais eux, saisis de stupeur et d'effroi, croyaient voir un esprit.
Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
38 Il leur dit: Pourquoi êtes-vous troublés, et pourquoi de telles pensées s'élèvent-elles dans vos coeurs?
Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
39 Voyez mes mains et mes pieds: c'est moi-même. Touchez-moi et regardez: un esprit n'a ni chair ni os, ce que j'ai, comme vous le voyez.
Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
40 En disant cela, il leur montra ses mains et ses pieds.
Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
41 Mais comme, dans leur joie, ils ne croyaient pas encore, et comme ils étaient remplis d'étonnement, il leur dit: Avez-vous ici quelque chose à manger?
Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
42 Ils lui présentèrent un morceau de poisson grillé.
Sai suka bashi gasasshen kifi.
43 Il le prit et le mangea en leur présence.
Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
44 Puis il leur dit: Voilà ce que je vous déclarais, quand j'étais encore avec vous, et quand je vous disais qu'il fallait que fût accompli tout ce qui est écrit à mon sujet dans la loi de Moïse, dans les prophètes et dans les psaumes.
Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
45 Alors il leur ouvrit l'esprit pour leur faire comprendre les Écritures.
Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
46 Et il leur dit: C'est ainsi qu'il est écrit que le Christ devait souffrir, qu'il ressusciterait des morts le troisième jour,
Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
47 et qu'on prêcherait en son nom la repentance, pour la rémission des péchés, parmi toutes les nations, en commençant par Jérusalem.
Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
48 Vous êtes témoins de ces choses;
Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
49 et moi, je vais vous envoyer ce que mon Père vous a promis. Quant à vous, demeurez dans la Ville, jusqu'à ce que vous soyez revêtus de la puissance d'en haut.
Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
50 Il les emmena ensuite jusqu'aux environs de Béthanie, et, levant ses mains, il les bénit.
Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
51 Pendant qu'il les bénissait, il se sépara d'eux et fut élevé au ciel.
Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
52 Eux, l'ayant adoré, s'en retournèrent à Jérusalem, pleins d'une grande joie.
Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
53 Ils se tenaient continuellement dans le temple, bénissant Dieu.
Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.

< Luc 24 >