< Jean 16 >
1 Je vous ai dit ces choses, pour que vous soyez préservés de toute chute.
“Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube.
2 On vous chassera des synagogues; et même, l'heure vient où quiconque vous fera mourir croira rendre un culte à Dieu.
Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.
3 Et ils feront cela, parce qu'ils n'ont connu ni le Père, ni moi.
Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba.
4 Mais je vous ai dit ces choses, afin que, quand l'heure sera venue, vous vous souveniez que je vous les ai dites. Je ne vous les ai pas dites dès le commencement, parce que j'étais avec vous.
Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku.” Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
5 Maintenant, je m'en vais auprès de Celui qui m'a envoyé, et aucun de vous ne me demande: Où vas-tu?
Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?'
6 Mais parce que je vous ai dit ces choses, la tristesse a rempli votre coeur.
Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku.
7 Cependant je vous dis la vérité: il vous est avantageux que je m'en aille! Car si je ne m'en vais pas, le Consolateur ne viendra point à vous; mais si je m'en vais, je vous l'enverrai.
Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 Et quand il sera venu, il convaincra le monde de péché, de justice et de jugement;
Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci.
9 de péché, parce qu'ils ne croient pas en moi;
Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba,
10 de justice, parce que je m'en vais auprès du Père, et que vous ne me verrez plus;
Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba,
11 de jugement, parce que le prince de ce monde est jugé.
game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
12 J'ai encore plusieurs choses à vous dire: mais elles sont maintenant au-dessus de votre portée.
“Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba.
13 Quand lui, l'Esprit de vérité, sera venu, il vous conduira dans toute la vérité; car il ne parlera pas de son chef, mais il dira tout ce qu'il aura entendu, et il vous annoncera les choses à venir.
Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru.
14 C'est lui qui me glorifiera, parce qu'il prendra de ce qui est à moi, et qu'il vous l'annoncera.
Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
15 Tout ce que possède le Père est à moi; c'est pourquoi, j'ai dit qu'il prendra de ce qui est à moi, et qu'il vous l'annoncera.
Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku.
16 Encore un peu de temps et vous ne me verrez plus; puis encore un peu de temps, et vous me verrez, parce que je vais auprès du Père.
“Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni.”
17 Alors, quelques-uns de ses disciples se dirent les uns aux autres: Qu'est-ce qu'il nous dit: Encore un peu de temps, et vous ne me verrez plus; puis encore un peu de temps, et vous me verrez; et aussi: Parce que je vais auprès du Père?
Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, “Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?”
18 Ils disaient donc: Que signifie ce qu'il dit: Un peu de temps? Nous ne savons de quoi il parle.
Saboda haka sukace, “Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba.”
19 Jésus, connaissant qu'ils voulaient l'interroger, leur dit: Vous vous demandez les uns aux autres ce que signifie cette parole: Encore un peu de temps, et vous ne me verrez plus; puis encore un peu de temps, et vous me verrez.
Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, “Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, “Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'?
20 En vérité, en vérité, je vous le déclare, vous pleurerez, vous vous lamenterez, et le monde se réjouira; vous serez dans la tristesse, mais votre tristesse sera changée en joie.
Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki.
21 Quand une femme enfante, elle est dans la douleur, parce que son heure est venue; mais quand l'enfant est né, elle ne se souvient plus de son angoisse, dans la joie qu'elle a de ce qu'un homme est né dans le monde.
Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
22 De même, vous êtes maintenant dans la douleur; mais je vous reverrai et votre coeur se réjouira, et personne ne vous ravira votre joie.
To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki.
23 En ce jour-là, vous ne m'interrogerez plus sur rien. En vérité, en vérité, je vous le déclare, ce que vous demanderez au Père, il vous le donnera en mon nom.
A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi.
24 Jusqu'à présent, vous n'avez rien demandé en mon nom. Demandez, et vous recevrez, afin que votre joie soit parfaite.
Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke.”
25 Je vous ai dit ces choses en similitudes. L'heure vient où je ne vous parlerai plus en similitudes, mais où je vous parlerai du Père ouvertement.
“Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
26 En ce jour-là, vous demanderez en mon nom, et je ne vous dis pas que je prierai le Père pour vous;
A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba,
27 car le Père lui-même vous aime, parce que vous m'avez aimé, et que vous avez cru que je suis venu de la part du Père.
domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito.
28 Je suis issu du Père, et je suis venu dans le monde; maintenant je quitte le monde, et je vais auprès du Père.
Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 Ses disciples lui dirent: C'est maintenant que tu parles ouvertement, et que tu ne dis pas de similitudes.
Almajiransa sukace, duba, “Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba!
30 Maintenant, nous savons que tu sais toutes choses, et que tu n'as pas besoin que personne t'interroge; voilà pourquoi nous croyons que tu es issu de Dieu.
Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”
31 Jésus leur répondit: Vous croyez maintenant?
Yesu ya amsa masu yace, “Ashe, yanzu kun gaskata?
32 Voici que l'heure vient, et elle est déjà venue, où vous serez dispersés, chacun de son côté, et où vous me laisserez seul; mais je ne serai pas seul, parce que le Père est avec moi.
Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni.
33 Je vous ai dit ces choses, afin que vous ayez la paix en moi. Vous aurez des afflictions dans le monde; mais prenez courage, j'ai vaincu le monde!
Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,”