< Actes 21 >

1 Après nous être séparés d'eux avec peine, nous nous embarquâmes, et nous vînmes droit à Cos, le jour suivant à Rhodes, et de là, à Patara.
Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
2 Il s'y trouvait un navire qui mettait à la voile pour la Phénicie; nous montâmes à son bord et nous partîmes.
Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
3 Quand nous fûmes en vue de l'île de Chypre, nous la laissâmes à gauche, poursuivant notre route vers la Syrie, et nous abordâmes à Tyr, parce que le navire devait y laisser son chargement.
Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
4 Étant allés trouver les disciples, nous restâmes sept jours avec eux. Poussés par l'Esprit, ils disaient à Paul de ne pas monter à Jérusalem.
Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
5 Mais, lorsque le temps de notre séjour fut écoulé, nous nous remîmes en route. Ils nous accompagnèrent tous, avec leurs femmes et leurs enfants, jusqu'en dehors de la ville; et, nous étant agenouillés sur le rivage, nous priâmes ensemble.
Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
6 Puis, après avoir fait nos adieux les uns aux autres, nous montâmes nous-mêmes à bord, tandis qu'ils retournaient chez eux.
Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
7 Quant à nous, achevant notre voyage par mer, nous nous rendîmes de Tyr à Ptolémaïs; et, après avoir salué les frères, nous passâmes un jour avec eux.
Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
8 Le lendemain, étant partis de là, nous vînmes à Césarée; et, entrant dans la maison de Philippe l'évangéliste, un des sept diacres, nous demeurâmes chez lui.
Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
9 Il avait quatre filles, non mariées, qui prophétisaient.
Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
10 Nous étions là depuis plusieurs jours, quand arriva de Judée un prophète, nommé Agabus.
Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
11 Étant venu nous voir, il prit la ceinture de Paul, se lia les pieds et les mains, et il dit: Voici ce que déclare le Saint-Esprit: L'homme à qui appartient cette ceinture sera ainsi lié à Jérusalem par les Juifs, et ils le livreront aux mains des Païens.
Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
12 Lorsque nous eûmes entendu ces paroles, les fidèles de ce lieu et nous, nous priâmes Paul de ne pas monter à Jérusalem.
Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
13 Mais il répondit: Que faites-vous, en pleurant ainsi et en me brisant le coeur? Car, pour moi, je suis prêt, non seulement à être lié, mais encore à mourir à Jérusalem pour le nom du Seigneur Jésus.
Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
14 Comme il ne se laissait pas persuader, nous n'insistâmes pas davantage, et nous dîmes: Que la volonté du Seigneur se fasse!
Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
15 Après ces jours-là, ayant fait nos préparatifs, nous montâmes à Jérusalem.
Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
16 Quelques disciples de Césarée y vinrent aussi avec nous, et ils nous conduisirent chez un certain Mnason, de Chypre, qui, depuis longtemps, était un disciple, et qui devait nous donner l'hospitalité.
Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
17 A notre arrivée à Jérusalem, les frères nous reçurent avec joie.
Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
18 Le lendemain, Paul se rendit avec nous chez Jacques; et tous les anciens s'y réunirent.
Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
19 Après les avoir salués, Paul raconta en détail ce que Dieu avait fait parmi les Païens par son ministère.
Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
20 Quand ils l'eurent entendu, ils glorifièrent Dieu. Puis ils lui dirent: Frère, tu vois combien de milliers de Juifs ont cru; et tous sont zélés pour la loi.
Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
21 Or, ils ont été informés que tu enseignes à tous les Juifs qui vivent parmi les Païens, de renoncer à Moïse, en leur disant qu'ils ne doivent pas circoncire leurs enfants, ni suivre leurs coutumes.
An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
22 Qu'y a-t-il donc à faire? Il est certain que la multitude va se rassembler; car on apprendra que tu es arrivé.
Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
23 Fais donc ce que nous allons te dire: Nous avons ici quatre hommes qui ont fait un voeu.
Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
24 Prends-les avec toi; purifie-toi avec eux, et charge-toi de ce qu'ils auront à payer pour se faire raser la tête. Tous sauront qu'il n'y a rien de vrai dans tout ce qu'on a raconté de toi, mais que, toi aussi, tu vis en observateur de la loi.
Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
25 Quant aux Païens qui ont cru, nous leur avons écrit ce que nous avions décidé: qu'ils devaient seulement s'abstenir des viandes offertes en sacrifice aux idoles, du sang, des animaux étouffés et de l'impudicité.
Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
26 Alors Paul, ayant pris ces hommes avec lui, et s'étant, dès le lendemain, purifié avec eux, entra dans le temple, pour déclarer le jour où la purification serait achevée et l'offrande présentée pour chacun d'eux.
Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
27 Les sept jours touchaient à leur fin, quand les Juifs d'Asie, ayant vu Paul dans le temple, ameutèrent toute la multitude et mirent la main sur lui,
Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
28 en criant: Hommes d'Israël, à l'aide! Voici l'homme qui prêche partout, à tout le monde, contre la nation, contre la loi et contre ce lieu; il a même introduit des Grecs dans le temple, et il a profané ce saint lieu!
Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
29 En effet, ils avaient vu auparavant Trophime d'Éphèse avec lui dans la ville, et ils croyaient que Paul l'avait introduit dans le temple.
Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
30 Toute la ville fut en émoi, et le peuple accourut en foule. Ayant saisi Paul, ils le traînèrent hors du temple, dont les portes furent aussitôt fermées.
Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
31 Comme ils cherchaient à le tuer, le bruit parvint au tribun de la cohorte que tout Jérusalem s'agitait.
Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
32 Immédiatement, il prit avec lui des soldats et des centeniers; et il se hâta de descendre vers eux. A la vue du tribun et des soldats, ils cessèrent de frapper Paul.
Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
33 Alors le tribun s'approcha, mit la main sur lui et ordonna de le lier de deux chaînes; puis, il demanda qui il était, et ce qu'il avait fait.
Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
34 Dans la foule, les uns criaient d'une manière, les autres d'une autre; et comme il ne pouvait rien apprendre de certain, à cause du tumulte, il ordonna de le mener dans la forteresse.
Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
35 Quand Paul fut sur les degrés, les soldats durent le porter, à cause de la violence de la foule.
Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
36 Car le peuple suivait en masse, en criant: A mort!
Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
37 Au moment d'entrer dans la forteresse, Paul dit au tribun: M'est-il permis de te dire quelque chose? Le tribun répondit: Tu sais parler grec?
An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
38 Tu n'es donc pas l'Égyptien qui, ces jours passés, a provoqué une sédition et entraîné au désert quatre mille brigands?
Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
39 Paul lui dit: Je suis Juif, de Tarse, citoyen d'une ville de Cilicie qui n'est pas sans renom; permets-moi, je te prie, de parler au peuple.
Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
40 Le tribun le lui permit; et Paul, se tenant sur les degrés, fit signe de la main au peuple. Un profond silence s'établit; puis, parlant en langue hébraïque, il leur dit:
Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,

< Actes 21 >