< Actes 18 >

1 Après cela, Paul, étant parti d'Athènes, vint à Corinthe.
Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti.
2 Il y trouva un Juif, nommé Aquilas, originaire du Pont, récemment arrivé d'Italie avec Priscille, sa femme, parce que Claude avait ordonné à tous les Juifs de s'éloigner de Rome; et il se joignit à eux.
A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu.
3 Comme Paul exerçait le même métier, il demeura chez eux, et ils travaillaient ensemble; or, leur métier était de faire des tentes.
Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.
4 Paul parlait dans la synagogue tous les jours de sabbat, et il persuadait les Juifs et les Grecs.
Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa.
5 Quand Silas et Timothée arrivèrent de Macédoine, Paul s'adonnait de toute son âme à la prédication, attestant aux Juifs que Jésus était le Christ.
Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne.
6 Mais, comme ils s'opposaient à lui et l'injuriaient, il secoua ses vêtements et leur dit: Que votre sang retombe sur votre tête! Pour moi, j'en suis net; dès maintenant, j'irai vers les Païens.
Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, “Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai.”
7 Etant sorti de là, il entra chez un certain Titius Justus, homme craignant Dieu et dont la maison touchait à la synagogue.
Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a.
8 Cependant Crispus, le chef de la synagogue, crut au Seigneur avec toute sa maison; et plusieurs des Corinthiens, ayant entendu Paul, crurent aussi et furent baptisés.
Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.
9 Le Seigneur dit à Paul pendant la nuit, dans une vision: Ne crains rien; mais parle et ne te tais point!
Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, “Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru.
10 Je suis avec toi, et personne ne mettra la main sur toi, pour te faire du mal; car j'ai un grand peuple dans cette ville.
Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin.”
11 Paul demeura là un an et six mois, enseignant parmi eux la parole de Dieu.
Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12 Lorsque Gallion était proconsul d'Achaïe, les Juifs, d'un commun accord, s'élevèrent contre Paul et l'amenèrent au tribunal, en disant:
Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a.
13 Cet homme excite les gens à adorer Dieu d'une manière contraire à la loi.
Suna cewa, “Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu.”
14 Comme Paul ouvrait la bouche pour répondre, Gallion dit aux Juifs: S'il s'agissait, ô Juifs, de quelque injustice ou de quelque crime, je vous écouterais patiemment, comme de raison.
Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, “Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta.
15 Mais puisqu'il s'agit de discussions sur une doctrine, sur des noms et sur votre loi particulière, examinez cela vous-mêmes; je ne veux pas être juge de ces choses.
Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku.”
16 Puis il les renvoya du tribunal.
Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a.
17 Alors tous, ayant saisi Sosthène, le chef de la synagogue, le battaient devant le tribunal; mais Gallion ne s'en souciait pas.
Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.
18 Paul resta encore quelque temps à Corinthe. Il prit ensuite congé des frères et s'embarqua pour la Syrie avec Priscille et Aquilas, après s'être fait raser la tête à Cenchrées; car il avait fait un voeu.
Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare.
19 Puis ils arrivèrent à Ephèse, où il laissa ses compagnons. Pour lui, il entra dans la synagogue et s'entretint avec les Juifs.
Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.
20 Alors ils lui demandèrent de rester plus longtemps, mais il n'y consentit pas.
Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba.
21 Il prit congé d'eux, en disant: Je reviendrai une autre fois chez vous, s'il plaît à Dieu; et il partit d'Éphèse.
Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, “In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana.” Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.
22 Étant débarqué à Césarée, il monta à Jérusalem; et, après avoir salué l'Église, il descendit à Antioche.
Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya.
23 Lorsqu'il y eut passé quelque temps, il en repartit, et il parcourut successivement la Galatie et la Phrygie, affermissant tous les disciples.
Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.
24 Cependant un Juif, nommé Apollos, natif d'Alexandrie, homme éloquent et très versé dans les Écritures, arriva à Éphèse.
A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah.
25 Il avait été instruit dans la voie du Seigneur; il parlait avec une grande ferveur, et il enseignait avec exactitude ce qui concerne Jésus, bien qu'il n'eût connaissance que du baptême de Jean.
Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai.
26 Il commença donc à parler avec hardiesse dans la synagogue. Priscille et Aquilas, l'ayant entendu, le prirent avec eux et lui exposèrent plus exactement encore la voie de Dieu.
Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.
27 Comme Apollos voulait passer en Achaïe, les frères l'y encouragèrent et écrivirent aux disciples de lui faire bon accueil. Quand il fut arrivé, il se rendit très utile, par la grâce de Dieu, à ceux qui avaient cru.
Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri.
28 Car il réfutait publiquement les Juifs avec une grande force, démontrant par les Écritures que Jésus est le Christ.
Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.

< Actes 18 >