< 1 Corinthiens 15 >
1 Je vous rappelle, frères, l'Évangile que je vous ai annoncé et que vous avez reçu, dans lequel aussi vous demeurez fermes,
Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita.
2 et par lequel vous êtes sauvés, si vous le retenez tel que je vous l'ai annoncé. — autrement, vous auriez cru en vain!
Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.
3 En effet, je vous ai transmis, avant toutes choses, cet enseignement que j'ai reçu moi-même: c'est que Christ est mort pour nos péchés, selon les Écritures;
Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi,
4 il a été enseveli; il est ressuscité le troisième jour, selon les Écritures;
cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.
5 il a été vu de Céphas, ensuite des Douze.
Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.
6 Après cela, il a été vu, en une seule fois, de plus de cinq cents frères, dont la plupart sont encore vivants aujourd'hui, et dont quelques-uns sont morts.
Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci.
7 Puis il a été vu de Jacques, et ensuite de tous les apôtres.
Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.
8 Enfin, après eux tous, il s'est aussi fait voir à moi, comme à je ne sais quel avorton.
A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini.
9 Car je suis le moindre des apôtres, moi qui ne suis pas digne d'être appelé apôtre, puisque j'ai persécuté l'Église de Dieu.
Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.
10 Mais c'est par la grâce de Dieu que je suis ce que je suis, et la grâce qu'il m'a faite n'a pas été vaine. Au contraire, j'ai travaillé beaucoup plus qu'eux tous, non pas moi pourtant, mais la grâce de Dieu qui est avec moi.
Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni.
11 Ainsi donc, que ce soit moi, que ce soit eux, voilà ce que nous prêchons et ce que vous avez cru.
Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.
12 Or, si l'on prêche que Christ est ressuscité des morts, comment quelques-uns d'entre vous peuvent-ils dire qu'il n'y a point de résurrection des morts?
To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu?
13 S'il n'y a point de résurrection des morts. Christ non plus n'est pas ressuscité.
Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan.
14 Et si Christ n'est pas ressuscité, notre prédication est donc vaine, et votre foi aussi est vaine.
idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.
15 Il se trouve même que nous sommes de faux témoins de Dieu, puisque nous avons témoigné, en contradiction avec Dieu, qu'il a ressuscité le Christ, — tandis qu'il ne l'a pas ressuscité, s'il est vrai que les morts ne ressuscitent pas.
Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba.
16 En effet, si les morts ne ressuscitent pas. Christ n'est pas non plus ressuscité.
Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan.
17 Et si Christ n'est pas ressuscité, votre foi est vaine; vous êtes encore dans vos péchés.
Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.
18 Alors aussi, ceux qui se sont endormis en Christ sont à jamais perdus.
To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan,
19 Si nous n'avons d'espérance en Christ que pour cette vie seulement, nous sommes les plus misérables de tous les hommes!
idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.
20 Mais maintenant, Christ est ressuscité des morts, et il est les prémices de ceux qui sont morts.
Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu.
21 En effet, puisque la mort est venue par un homme, c'est par un homme aussi qu'est venue la résurrection des morts.
Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.
22 Comme tous meurent en Adam, de même tous revivront en Christ,
Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka.
23 mais chacun à son propre rang: Christ est les prémices; puis ceux qui sont à Christ ressusciteront à son avènement.
Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.
24 Ensuite viendra la fin, quand il remettra le royaume à Dieu, le Père, après avoir détruit tout empire, toute domination et toute puissance;
Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko.
25 car il faut qu'il règne, jusqu'à ce qu'il ait mis tous ses ennemis sous ses pieds.
Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa.
26 — L'ennemi qui sera détruit le dernier, c'est la mort. —
Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.
27 Dieu, en effet, a mis toutes choses sous ses pieds; mais quand il est dit que toutes choses lui sont soumises, il est évident qu'il faut excepter Celui qui lui a soumis toutes choses.
Domin “yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” Amma da aka ce” yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba.
28 Puis, quand toutes choses lui auront été soumises, alors le Fils lui-même sera soumis à Celui qui lui a soumis toutes choses, afin que Dieu soit tout en tous.
Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.
29 Autrement, que feraient ceux qui se font baptiser pour les morts? Si absolument les morts ne ressuscitent pas, pourquoi se font-ils baptiser pour eux?
ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su?
30 Et pourquoi nous-mêmes sommes-nous à toute heure en péril?
Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?
31 Je suis chaque jour exposé à la mort, aussi vrai, frères, que vous êtes pour moi un sujet de gloire en Jésus-Christ, notre Seigneur.
Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
32 Si c'est dans des vues humaines que j'ai combattu contre les bêtes à Éphèse, quel avantage m'en revient-il? Si les morts ne ressuscitent pas, mangeons et buvons, car demain nous mourrons!.
Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? “bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu.”
33 Ne vous y trompez pas: les mauvaises compagnies corrompent les bonnes moeurs.
Kada fa a yaudare ku, domin “tarayya da mugaye takan bata halayen kirki.”
34 Revenez à la raison, comme il convient, et ne péchez point; car il y en a qui n'ont aucune connaissance de Dieu, je le dis à votre honte.
“Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.
35 Mais quelqu'un dira: Comment les morts ressuscitent-ils, et avec quel corps reviennent-ils?
Amma wani zaya ce, “Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi?
36 Insensé, ce que tu sèmes ne reprend pas vie, si d'abord il ne meurt.
Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.
37 Et quant à ce que tu sèmes, ce n'est pas le corps qui naîtra, que tu sèmes, mais un simple grain, de blé peut-être, ou de quelque autre semence.
Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban.
38 Et Dieu lui donne le corps qu'il a trouvé bon de lui donner, à chaque semence le corps qui lui est propre.
Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin.
39 Toute chair n'est pas la même chair; mais autre est la chair des hommes, autre la chair des bêtes, autre celle des oiseaux, autre celle des poissons.
Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.
40 Il y a aussi des corps célestes et des corps terrestres; mais l'éclat des corps célestes est différent de celui des corps terrestres.
Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce.
41 Autre est l'éclat du soleil, autre l'éclat de la lune, autre l'éclat des étoiles; et même une étoile diffère en éclat d'une autre étoile.
Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.
42 Il en est ainsi de la résurrection des morts. Le corps est semé corruptible, il ressuscite incorruptible;
Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne.
43 il est semé méprisable, il ressuscite glorieux; il est semé infirme, il ressuscite plein de force;
An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko.
44 il est semé corps animal, il ressuscite corps spirituel. S'il y a un corps animal, il y a aussi un corps spirituel;
An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.
45 c'est ainsi qu'il est écrit: «Le premier homme, Adam, a été fait âme vivante» Le dernier Adam est esprit vivifiant.
Haka kuma aka rubuta, “Adamu na farko ya zama rayayyen taliki.” Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai.
46 Mais ce n'est pas ce qui est spirituel qui vient le premier, c'est ce qui est animal; ce qui est spirituel vient ensuite.
Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.
47 Le premier homme, étant de la terre, est terrestre; le second homme est du ciel.
Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake.
48 Tel est le terrestre, tels sont aussi les terrestres; tel est le céleste, tels sont aussi les célestes.
kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama.
49 Et comme nous avons porté l'image de celui qui est terrestre, nous porterons aussi l'image de celui qui est. céleste.
Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.
50 Ce que j'affirme, frères, c'est que la chair et le sang ne peuvent hériter le royaume de Dieu, et que la corruption n'hérite point l'incorruptibilité.
To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba.
51 Voici un mystère que je vous révèle: nous ne mourrons pas tous, mais tous nous serons changés,
Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.
52 en un instant, en un clin d'oeil, au son de la dernière trompette; car la trompette sonnera, et les morts ressusciteront incorruptibles, et nous serons changés.
Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu.
53 Il faut, en effet, que ce corps corruptible revête l'incorruptibilité, et que ce corps mortel revête l'immortalité.
Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.
54 Et quand ce corps corruptible aura revêtu l'incorruptibilité, et que ce corps mortel aura revêtu l'immortalité, alors s'accomplira cette parole de l'Ecriture: «La mort a été engloutie dans la victoire.»
Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, “An hadiye mutuwa cikin nasara.”
55 mort, où est ta victoire? mort, où est ton aiguillon? (Hadēs )
“Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
56 Or, l'aiguillon de la mort, c'est le péché; et la puissance du péché, c'est la loi.
Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce.
57 Mais grâces soient rendues à Dieu, qui nous donne la victoire par notre Seigneur Jésus-Christ!
Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!
58 Ainsi donc, mes frères bien-aimés, soyez fermes, inébranlables, et abondez toujours plus dans l'oeuvre du Seigneur, sachant que votre travail n'est pas vain auprès du Seigneur.
Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.