< Luc 20 >

1 Un de ces jours-là, comme il instruisait le peuple dans le Temple et lui annonçait l'Évangile, survinrent les chefs des prêtres et les Scribes, réunis aux Anciens,
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 qui lui tinrent ce langage: «Dis-nous en vertu de quelle autorité tu fais ces choses, ou qui est celui qui t'a donné cette autorité?»
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 Il leur fit cette réponse: «Je vous poserai, moi aussi, une question: répondez-moi;
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 le baptême de Jean venait-il du ciel ou des hommes?»
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 Or ils faisaient, à part eux, ce raisonnement: «Si nous disons: du ciel, il répliquera: «Pourquoi alors ne l'avez-vous pas cru?»
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 Si nous disons: des hommes, tout le peuple nous lapidera; car il est convaincu que Jean était un prophète.»
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 Ils répondirent donc qu'ils ne savaient d'où venait ce baptême.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 Et Jésus leur répondit à son tour: «Je ne vous dis pas, moi non plus, en vertu de quelle autorité je fais ces choses.»
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 Puis il se mit à raconter au peuple cette parabole: «Un homme planta une vigne, la loua à des vignerons et fit une longue absence.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 La saison venue, il envoya un serviteur aux vignerons, chargé de recevoir le produit de la vigne. Les vignerons, après l'avoir battu, le renvoyèrent les mains vides.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 Le maître alors leur envoya un autre serviteur. Celui-là, ils le battirent aussi, le traitèrent avec mépris et le renvoyèrent les mains vides.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 Il leur en envoya un troisième. Celui-là ils le couvrirent de blessures et le jetèrent dehors.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 — «Que dois-je faire?» dit alors le maître de la vigne. «Je leur enverrai mon fils, mon bien-aimé; sans doute, ils le respecteront.»
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 Mais quand les vignerons le virent, ils firent entre eux ce raisonnement: Celui-là c'est l'héritier; tuons-le pour que l'héritage soit à nous.»
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 Alors ils le jetèrent hors de la vigne et le tuèrent. Que leur fera donc le maître de la vigne?
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 Il viendra, il fera périr ces vignerons et donnera la vigne, à d'autres.» — «Que cela n'arrive pas!» dirent-ils à ces paroles.
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 Mais lui, les regardant en face, ajouta: «Qu'est-ce donc que ce passage de l'Écriture: «La pierre qu'ont rejetée ceux qui bâtissaient; Celle-là même est devenue la tête de l'angle.»
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 «Quiconque tombera sur cette pierre s'y brisera; et celui sur qui elle tombera, elle le mettra en poussière.»
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 Les Scribes et les chefs des prêtres cherchèrent à mettre immédiatement la main sur lui; car ils comprenaient bien que c'était eux qu'il avait en vue dans cette parabole; mais ils redoutaient le peuple.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 Ils le surveillèrent et lui envoyèrent d'habiles espions qui faisaient semblant d'être de bonne foi; leur but était de surprendre une parole de lui qui leur permît de le livrer aux autorités et au pouvoir du procurateur.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 Ils lui posèrent une question: «Maître, nous savons que tu es droit dans ta parole et dans ton enseignement, que tu ne fais acception de personne, que, tout au contraire, tu enseignes en toute vérité la voie de Dieu.
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 Nous est-il permis, oui ou non, de payer un tribut à César?»
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 Devinant leur ruse, Jésus leur dit:
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 «Montrez-moi un denier... De qui porte-t-il l'image et l'inscription?» — «De César», répondirent-ils. —
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 «Eh bien, leur dit-il alors, rendez à César ce qui est à César et à Dieu ce qui est à Dieu.»
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 Il leur fut ainsi impossible de surprendre une parole de lui en présence du peuple, et tout étonnés de cette réponse, ils gardèrent le silence.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 Survinrent ensuite quelques Saducéens (ceux qui affirment qu’il n’y a point de résurrection); ils lui posèrent aussi une question:
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 «Maître, dirent-ils, voici ce que Moïse nous a prescrit: «Si le frère de quelqu'un meurt laissant une femme sans enfants, celui-ci devra épouser la veuve, pour susciter à son frère une postérité.»
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 Or, il y a eu sept frères. Le premier a pris femme et est mort sans enfants.
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
30 Le second a épousé la veuve;
Na biyun,
31 puis le troisième; tous les sept; aucun n'a laissé d'enfants; et tous sont morts.
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 Enfin, la femme aussi est morte.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 Eh bien, à la résurrection, duquel d'entre eux cette femme sera-t-elle l'épouse? Les sept, en effet, l'ont eue pour femme.»
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 Jésus leur répondit: «Les enfants de ce monde se marient et donnent en mariage; (aiōn g165)
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
35 mais ceux qui ont été jugés dignes de participer au monde à venir et à la résurrection d'entre les morts, ne se marient, ni ne sont donnés en mariage; (aiōn g165)
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
36 car ils ne peuvent plus mourir: ils sont semblables aux anges, et ils sont fils de Dieu étant fils de la résurrection.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 Or que les morts ressuscitent, Moïse l'a montré au passage du buisson, quand il appelle le Seigneur, le Dieu d'Abraham, le Dieu d'Isaac, le Dieu de Jacob.
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 Or ce n'est point de morts, c'est de vivants qu'il est Dieu. Pour lui ils vivent tous.»
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 Quelques Scribes intervinrent pour dire: «Maître, tu as parfaitement répondu.»
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 Personne n'osait plus lui poser une seule question.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 Il leur demanda alors: «Comment dit-on que le Christ est Fils de David,
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 quand David dit lui-même au livre des Psaumes: «Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Siège à ma droite;
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 Jusqu'à ce que j'aie mis tes ennemis sous tes pieds.»
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 Ainsi David l'appelle Seigneur, comment donc est-il son fils?»
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 Devant tout le peuple qui entendait, il dit aux disciples:
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 «Soyez sur vos gardes avec les Scribes qui se complaisent à se promener en robes solennelles, qui aiment à recevoir des salutations sur les places publiques, à occuper les premiers sièges dans les synagogues, les premières places dans les festins,
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 qui dévorent, les ressources des veuves, et qui affectent de prier longuement. C'est pour ces hommes-là que le jugement aura le plus de rigueur.»
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”

< Luc 20 >