< Psaumes 88 >

1 Cantique des fils de Coré. Au maître chantre. A chanter avec les luths. Hymne de Héman Esrahite. Éternel, mon Dieu sauveur, je crie à toi et le jour et la nuit:
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 qu'à toi parvienne ma prière; prête l'oreille à ma supplication!
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Car mon âme est rassasiée de malheur, et ma vie penche vers les Enfers. (Sheol h7585)
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
4 Je suis assimilé à ceux qui descendent dans la fosse, je suis comme un homme sans force;
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 ma couche est entre les morts, je suis tel que les morts gisants dans le tombeau, auxquels tu ne penses plus, et qui ne sont plus à portée de ta main.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Tu m'as jeté dans une fosse profonde, dans des ténèbres, dans des abîmes.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Ton courroux pèse sur moi, et de tous tes flots tu m'as accablé. (Pause)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Tu as éloigné de moi ceux que je connais, tu m'as rendu pour eux un objet d'horreur; enveloppé, je ne trouve point d'issue.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mes yeux fondent par l'effet du malheur; Éternel, je t'invoque chaque jour, et je tends mes mains vers toi.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Pour les morts feras-tu des miracles? Les ombres se lèveront-elles pour te louer? (Pause)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Dans le tombeau parle-t-on de ta grâce, et de ta fidélité, dans le séjour de la mort?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Dans les ténèbres tes miracles sont-ils remarqués, et ta justice, dans la région de l'oubli?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Je t'implore donc, Éternel, et dès le matin ma prière te prévient.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Éternel, pourquoi me rejettes-tu, et me caches-tu ta face?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Je suis malheureux et mourant dès ma jeunesse, je subis les terreurs et je suis éperdu.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Ton courroux m'assaille, tes frayeurs m'anéantissent,
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 m'enveloppent, comme des eaux, tout le jour, me cernent toutes à la fois.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Tu as éloigné de moi amis et compagnons, et ceux que je connais, me sont invisibles.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.

< Psaumes 88 >