< Psaumes 83 >

1 Cantique d'Asaph. O Dieu, ne garde pas le silence, ne sois point sourd, ne te tiens pas en repos, ô Dieu!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Car voici, tes ennemis sont en rumeur, et ceux qui te haïssent, lèvent la tête;
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 ils trament contre ton peuple un astucieux complot, et se concertent contre tes protégés.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Ils disent: « Sus! exterminons-les du milieu des peuples, que le nom d'Israël ne soit plus rappelé désormais! »
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Car ils se concertent d'un commun accord, ils font alliance contre toi:
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 ce sont les tentes d'Edom et des Ismaëlites, Moab et les Hagariens,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal et Amman et Amalek, la Philistie avec les habitants de Tyr;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Assur aussi s'unit à eux, et prête son bras aux enfants de Lot. (Pause)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Traite-les comme Madian, comme Sisera, comme Jabin au torrent de Kison,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 qui furent défaits à En-Dor, et fumèrent le sol!
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Rends-les, rends leurs princes pareils à Horeb et à Zéeb, et tous leurs rois, à Zébah et Tsalmunah;
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 car ils disent: « Rendons-nous maîtres des demeures de Dieu! »
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Mon Dieu, assimile-les au tourbillon, à la balle livrée au vent,
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 au feu qui dévore la forêt, et à la flamme qui embrase la montagne!
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 Ainsi, poursuis-les de ta tempête, et terrifie-les par ton ouragan!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Couvre leur visage de honte, afin qu'ils s'enquièrent de ton nom, Éternel!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Qu'ils soient confondus et terrifiés pour toujours, et qu'ils périssent avec ignominie!
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 afin qu'ils sachent que ton nom, Etemel, ton nom seul est souverain sur toute la terre.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Psaumes 83 >