< Psaumes 47 >
1 Au maître chantre. Des fils de Coré. Cantique. Vous tous les peuples, battez des mains! éclatez pour Dieu en acclamations!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
2 Car l'Éternel, le Très-haut, est digne de crainte, Il est le grand Roi de toute la terre.
Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
3 Il a rangé des peuples sous nos lois, et mis des nations sous nos pieds;
Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
4 Il nous a choisi lui-même notre héritage, orgueil de Jacob qu'il aime. (Pause)
Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
5 Dieu arrive avec des acclamations, et l'Éternel s'avance au son de la trompette.
Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
6 Chantez l'Éternel, chantez! Chantez à notre Roi, chantez!
Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
7 Car Dieu est Roi de toute la terre: chantez-lui des hymnes!
Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
8 Dieu règne sur les peuples; Dieu est assis sur son trône saint.
Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
9 Les princes des peuples se réunissent au peuple du Dieu d'Abraham; car les boucliers de la terre sont à Dieu, Il est souverainement élevé.
Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.