< Psaumes 138 >
1 De David. Je veux Te louer de tout mon cœur, et te célébrer en la présence de Dieu;
Ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; a gaban “alloli” zan rera yabo.
2 me prosterner dans ton saint temple, et louer ton nom, car tu es bon et fidèle! Tu as donné à ta promesse des effets qui dépassent toute ta renommée.
Zan rusuna ta wajen haikalinka mai tsarki zan kuma yabi sunanka saboda ƙaunarka da amincinka, saboda ka ɗaukaka a bisa kome sunanka da kuma maganarka.
3 Quand je criai, tu m'exauças, tu m'enhardis, donnant force à mon âme.
Sa’ad da na kira, ka amsa mini; ka sa na zama mai ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa ni.
4 Éternel, tous les rois de la terre te loueront, à l'ouïe des promesses sorties de ta bouche;
Bari dukan sarakunan duniya su yabe ka, ya Ubangiji, sa’ad da suka ji maganganun bakinka.
5 et ils célébreront les voies de l'Etemel, car la gloire de l'Éternel est grande.
Bari su rera game da hanyoyin Ubangiji, gama ɗaukakar Ubangiji da girma take.
6 L'Éternel est élevé, Il découvre l'humble, et de loin Il reconnaît le superbe.
Ko da yake Ubangiji yana bisa, yakan dubi kāsassu, amma tun da nesa ya san masu girman kai.
7 Si je chemine au milieu des angoisses, tu me redonnes la vie, tu opposes ta main à la fureur de mes ennemis, et ta droite me délivre.
Ko da na yi tafiya a tsakiyar wahala, kana kiyaye raina; ka miƙa hannunka a kan fushin maƙiyana, da hannunka na dama ka cece ni.
8 L'Éternel agira pour moi jusques au bout. Seigneur, ta miséricorde est éternelle, ne laisse pas tomber les œuvres de tes mains!
Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.