< Psaumes 132 >
1 Cantique graduel. Éternel, souviens-toi de David, et de toutes ses tribulations!
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 Il fit à l'Éternel ce serment, ce vœu au Dieu puissant de Jacob:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 « Je ne rentre point sous le toit de ma maison, et je ne monte point vers le lit où je repose;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 je n'accorde ni le dormir à mes yeux, ni le sommeil à mes paupières,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 que je n'aie trouvé un séjour pour l'Éternel, une demeure pour le Dieu puissant de Jacob. »
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Voici, nous apprenions qu'elle était à Ephrata, puis nous la trouvions dans les champs de Jahar.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Rendons-nous à Sa demeure, prosternons-nous devant Son marchepied!
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Lève-toi, Éternel, viens à ton lieu de repos, toi, et l'arche de ta majesté!
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Que tes prêtres soient vêtus de la grâce, et que tes saints poussent des cris de joie!
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 Pour l'amour de David, ton serviteur, ne rebute pas ton Oint!
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 L'Éternel fit à David un serment véridique, Il n'en reviendra point: « Je mettrai sur ton trône un fruit de tes entrailles.
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Si tes fils gardent mon alliance et les lois que je leur enseigne, leurs enfants aussi à jamais seront assis sur ton trône. »
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Oui, l'Éternel a fait choix de Sion, Il veut y fixer sa demeure.
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 « C'est ici pour jamais le lieu de mon repos, je veux y demeurer, car je l'ai choisie.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Je veux bénir sa nourriture, et rassasier de pain ses indigents.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Et je revêtirai ses prêtres de salut, et ses saints pousseront des cris de joie.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Là j'élèverai la puissance de David, et je tiendrai devant mon Oint un flambeau.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Je revêtirai ses ennemis d'opprobre, et sur sa tête son diadème brillera. »
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”