< Psaumes 106 >

1 Alléluia! Louez l'Éternel, car Il est bon, car sa miséricorde est éternelle!
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qui saura exprimer les exploits de l'Éternel, et énoncer sa louange tout entière?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Heureux ceux qui observent la loi, et pratiquent la justice en tout temps!
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Pense à moi, Seigneur, en étant propice à ton peuple, viens à moi avec ton secours!
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 afin que, témoin du bonheur de tes élus, je me réjouisse de la joie de ton peuple, que je me glorifie avec ton héritage.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Nous avons péché de même que nos pères, nous avons été pervers et impies.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Nos pères en Egypte ne réfléchirent point à tes miracles, ne se rappelèrent point le nombre de tes grâces, et ils se rebellèrent près de la mer, la mer des algues.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Mais Il les délivra pour l'amour de son nom, afin de faire connaître sa puissance.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Et Il tança la mer des algues, et elle se dessécha, et Il leur fit traverser les flots comme le désert.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Et Il les sauva de la main de l'adversaire, et les racheta de la main de l'ennemi;
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 et les eaux recouvrirent leurs oppresseurs, il n'en resta pas un seul.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Alors ils crurent à ses paroles, ils chantèrent ses louanges.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Ils furent prompts à oublier ses exploits, et ne surent pas attendre ses dispensations;
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 et ils conçurent une convoitise dans le désert, et tentèrent Dieu dans la solitude.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Alors Il condescendit à leur demande, mais Il leur envoya aussi la consomption.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Et ils furent jaloux de Moïse dans le camp, d'Aaron, le saint de l'Éternel.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 Alors la terre s'ouvrit et engloutit Dathan, et recouvrit la troupe d'Abiram,
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 et un feu s'alluma au milieu de leur troupe, et des flammes consumèrent les sacrilèges.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Ils fabriquèrent un veau en Horeb, et adorèrent une image de fonte,
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 et ils échangèrent leur gloire contre l'effigie d'un bœuf qui broute l'herbe.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Ils oublièrent Dieu, leur libérateur, qui avait opéré de grandes choses en Egypte,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 des miracles dans la terre de Cham, des prodiges sur la mer des algues.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Alors Il pensait à les détruire, si Moïse, son élu, ne s'était mis à la brèche devant Lui, pour détourner sa colère de détruire.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Et ils se dégoûtèrent du pays des délices; ils ne croyaient pas à ses promesses;
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 et ils murmurèrent dans leurs tentes, ne furent point dociles à la voix de l'Éternel.
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Alors levant sa main Il jura de les coucher dans le désert,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 et de jeter leur race au milieu des nations, et de les disséminer dans tous les pays.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Et ils s'attachèrent à Baal-Pehor, et mangèrent les sacrifices des morts,
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 et L'irritèrent par leurs crimes: aussi un fléau fit irruption chez eux.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Alors parut Phinées qui fit justice, et le fléau fut arrêté:
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 et cela lui fut imputé à justice, d'âge en âge, éternellement.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Et ils Le provoquèrent aux Eaux de la Querelle, et Moïse eut à souffrir à cause d'eux;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 car ils résistèrent à sa volonté, et les paroles de ses lèvres furent inconsidérées.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Ils ne détruisirent point les peuples que l'Éternel leur avait signalés;
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 et ils se mêlèrent avec les peuples, et apprirent leur façon de faire;
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 et ils servirent leurs idoles, qui leur furent un piège;
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 ils immolèrent leurs fils et leurs filles aux idoles,
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 et répandirent le sang innocent, le sang de leurs fils et de leurs filles, qu'ils immolèrent aux idoles de Canaan; et le pays fut profané par des meurtres;
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 et ils se souillèrent avec leurs œuvres, et leur conduite fut une prostitution.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Alors la colère de l'Éternel s'alluma contre son peuple, et son héritage devint son abomination;
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 et Il les livra aux mains des peuples, et leurs ennemis furent leurs maîtres;
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 et ils furent opprimés par leurs adversaires, et plièrent sous leur main.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Nombre de fois Il les délivra; mais ils regimbèrent, ne prenant conseil que d'eux-mêmes, et ils se perdirent par leur faute.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Et Il regarda vers eux pendant la détresse, quand Il entendit leurs gémissements;
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 et Il se ressouvint pour eux de son alliance, et céda à la pitié dans sa grande miséricorde,
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 et Il leur fit rencontrer de la compassion auprès de tous ceux qui les tenaient captifs.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sois-nous en aide, Éternel, notre Dieu, et recueille-nous du milieu des peuples, pour que nous chantions ton saint nom, et que nous fassions gloire de te louer!
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Béni soit l'Éternel, Dieu d'Israël, de l'éternité à l'éternité! et que tout le peuple dise: Ainsi soit-il! Alleluia!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psaumes 106 >