< Proverbes 3 >

1 Mon fils, n'oublie pas mes leçons, et que ton cœur garde mes préceptes!
Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,
2 Car ils prolongeront tes jours et tes années de vie, et te donneront la paix.
gama za su ƙara maka tsawon rai da shekaru masu yawa su kuma kawo maka wadata.
3 Que l'amour et la vérité ne te quittent pas; lie-les à ton col, écris-les sur les tablettes de ton cœur!
Kada ka bar ƙauna da aminci su rabu da kai; ka ɗaura su kewaye da wuyanka, ka rubuta su a allon zuciyarka.
4 Alors tu trouveras grâce et bon succès devant Dieu et devant les hommes.
Sa’an nan za ka sami tagomashi da kuma suna mai kyau a gaban Allah da kuma a gaban mutane.
5 Confie-toi en Dieu de tout ton cœur, et ne t'appuie pas sur ton propre sens!
Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;
6 En toutes tes voies regarde vers Lui, et Il aplanira tes sentiers.
cikin dukan hanyoyinka ka amince da shi, zai kuwa sa hanyoyinka su miƙe.
7 Ne sois point sage à tes propres yeux; crains l'Éternel, et fuis le mal!
Kada ka zama mai hikima a ganinka; ka ji tsoron Ubangiji ka kuma guji mugunta.
8 ce sera la santé de ton corps, et le rafraîchissement de tes os.
Wannan zai ba wa jikinka lafiya yă kuma adana ƙasusuwanka.
9 Honore Dieu avec ta richesse, et avec les prémices de tout ton revenu!
Ka girmama Ubangiji da dukan dukiyarka, ta wurin miƙa masa nunan fari na dukan amfanin gonarka;
10 et tes greniers se rempliront d'abondance, et de moût tes cuves regorgeront.
ta haka rumbunanka za su cika har su zuba, randunanka kuma su cika har baki da sabon ruwan inabi.
11 Ne méprise pas, mon fils, la correction de l'Éternel, et ne t'irrite point de ses châtiments!
Ɗana, kada ka rena horon Ubangiji kada kuma ka ƙi tsawatawarsa,
12 Car c'est celui qu'il aime que l'Éternel châtie, comme un père l'enfant auquel il prend plaisir.
domin Ubangiji yakan hori waɗanda yake ƙauna, kamar yadda mahaifi yake yin wa ɗa da yake fariya da shi.
13 Heureux l'homme qui trouve la sagesse, et l'homme qui obtient la prudence!
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14 Car son acquisition vaut mieux que celle de l'argent, et ce qu'elle rapporte, est meilleur que l'or fin;
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15 elle a plus de prix que les perles, et tout ce que tu as de précieux ne lui équivaut pas.
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16 Longue vie est dans sa main droite; dans sa gauche, richesse et honneur.
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17 Ses voies sont des voies de délices, et tous ses sentiers sont des sentiers de paix.
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18 Elle est un arbre de vie pour ceux qui la saisissent, et qui la tient ferme en est rendu heureux.
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19 Par la sagesse l'Éternel a fondé la terre, et élevé les Cieux par son intelligence;
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20 par sa science Il ouvrit les abîmes, et fit des nues distiller la rosée.
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21 Mon fils, ne les perds pas de vue, garde la sagesse et la réflexion!
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22 Elles donneront vie à ton âme, et parure gracieuse à ton col.
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23 Alors d'un pas sûr tu marcheras dans ta voie, et ton pied ne heurtera point.
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24 En te couchant tu seras sans peur, et couché tu auras un doux sommeil.
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25 Ne redoute pas l'alarme soudaine, ni l'attaque des méchants qui surviendrait;
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26 car l'Éternel sera ton assurance, et Il empêchera ton pied d'être pris dans le piège.
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
27 Ne refuse pas un bienfait à celui qui y a droit, quand tu as le pouvoir de l'accorder.
Kada ka ƙi yin alheri ga duk wanda ya dace, sa’ad da kana iya yin haka.
28 Ne dis pas à ton prochain: « Va-t'en et reviens, demain je te donnerai! » quand tu as de quoi donner.
Kada ka ce wa maƙwabcinka “Ka yă dakata sai gobe,” idan kana iya taimakonsa yanzu.
29 Ne machine pas du mal contre ton prochain, qui habite en confiance auprès de toi.
Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, wanda yake zama da aminci kusa da kai.
30 N'entre avec personne en procès sans cause, quand tu n'as pas été provoqué par un tort.
Kada ka zargi mutum ba dalili, sa’ad da bai yi laifi ba.
31 Ne porte pas envie à l'homme violent, et ne choisis aucune de ses voies,
Kada ka ji kishin mai tā-da-na-zaune-tsaye ko ka yi sha’awar aikata ayyukansu.
32 car l'homme faux est l'abomination de l'Éternel, mais aux hommes droits Il donne son amitié.
Gama Ubangiji yana ƙyama mai aikata mugunta amma yakan rungumi adalin da ya amince da shi.
33 La malédiction de l'Éternel est sur la maison de l'impie, mais Il bénit la demeure des justes.
La’anar Ubangiji tana a gidan mugaye, amma yakan albarkaci gidan adali.
34 S'il se moque des moqueurs, aux humbles Il accorde sa grâce.
Yakan yi wa masu girman kai ba’a amma yakan yi wa mai sauƙinkai alheri.
35 Les sages ont l'honneur pour héritage, mais les insensés recueillent la honte.
Masu hikima sukan sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

< Proverbes 3 >