< Marc 3 >
1 Et il entra de nouveau dans une synagogue, et il se trouvait là un homme ayant la main desséchée.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 Et ils l'observaient pour voir si, le jour du sabbat, il le guérirait, afin de pouvoir l'accuser.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 Et il dit à l'homme qui avait la main sèche: « Lève-toi, et viens ici au milieu. »
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 Et il leur dit: « Est-il permis le jour du sabbat de faire du bien ou de faire du mal, de sauver une vie ou de la détruire? » Mais eux se taisaient.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 Et ayant porté tout autour de lui ses regards sur eux avec colère, étant vivement attristé de l'endurcissement de leur cœur, il dit à l'homme: « Étends la main. » Et il l'étendit et sa main fut guérie.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 Et les pharisiens étant sortis tenaient aussitôt conseil contre lui avec les Hérodiens, afin de le faire mourir.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Et Jésus se retira, avec ses disciples vers la mer, et une multitude nombreuse venue de la Galilée le suivit. Et de la Judée,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 et de Jérusalem, et de l'Idumée, et d'au delà le Jourdain, et des environs de Tyr et de Sidon, une multitude nombreuse entendant parler de tout ce qu'il faisait, vint à lui.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 Et il dit à ses disciples de faire tenir près de lui des barques, à cause de la foule, afin qu'on ne se pressât pas contre lui;
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 en effet il avait guéri beaucoup de monde, en sorte que tous ceux qui avaient des infirmités se jetaient sur lui, afin de le toucher.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 Et les esprits impurs, quand ils le voyaient, se jetaient à ses pieds et s'écriaient: « Tu es le fils de Dieu. »
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 Et il leur adressait beaucoup de remontrances, pour qu'ils ne le fissent pas connaître.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 Et il monte sur la montagne, et il appelle à lui ceux qu'il voulait; et ils vinrent vers lui.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 Et il en désigna douze, qu'il nomma aussi apôtres, afin qu'ils fussent avec lui, et afin de les envoyer prêcher,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 en ayant l'autorité de chasser les démons.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 Et il désigna les douze, et il donna à Simon le nom de Pierre,
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 et Jacques fils de Zébédée et Jean le frère de Jacques, et il leur donna le nom de Boanerges, qui signifie fils du tonnerre,
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 et André, et Philippe, et Barthélémy, et Matthieu, et Thomas, et Jacques le fils d'Alphée, et Thaddée, et Simon le Cananéen,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 et Judas Iscarioth, lequel aussi le livra.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Et il se rend à la maison, et la foule se réunit de nouveau, en sorte qu'ils ne pouvaient pas même prendre leur repas.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 Et ceux qui lui tenaient de près l'ayant appris sortirent pour se saisir de lui, car ils disaient: « Il a perdu l'esprit. »
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 Et les scribes descendus de Jérusalem disaient: « Il a Béézéboul, » et: « C'est par le chef des démons qu'il chasse les démons. »
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 Et les ayant appelés à lui, il leur disait sous forme de paraboles: « Comment Satan peut-il chasser Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 Et si un royaume est divisé contre lui-même, ce royaume-là ne peut pas subsister;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison-là ne pourra pas subsister;
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 et si Satan s'est soulevé contre lui-même et est divisé, il ne peut pas subsister, mais il prend fin.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Mais personne ne peut, après être entré dans la maison de l'homme fort, piller ses biens, s'il n'a pas premièrement garrotté l'homme fort, et alors il pillera sa maison.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 En vérité je vous déclare que tous les péchés et les blasphèmes, qu'ils auront pu proférer, seront pardonnés aux fils des hommes;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 mais celui qui aura blasphémé contre l'esprit saint n'a point de pardon à attendre pour l'éternité, mais il est coupable d'un péché éternel. » (aiōn , aiōnios )
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn , aiōnios )
30 C'est qu'ils disaient: « Il a un esprit impur. »
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 Et sa mère et ses frères viennent, et se tenant debout dehors ils envoyèrent vers lui pour l'appeler.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 Et la foule était-assise autour de lui, et on lui dit: « Voici, ta mère et tes frères sont dehors qui te cherchent. »
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 Et il leur réplique: « Qui est ma mère et mes frères? »
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Ayant porté ses regards tout alentour sur ceux qui étaient assis en cercle autour de lui, il dit: « Voilà ma mère et mes frères;
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 quiconque aura fait les volontés de Dieu, celui-là est mon frère, et ma sœur, et ma mère. »
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”