< Josué 20 >
1 Et l'Éternel parla à Josué en ces termes:
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 Parle aux enfants d'Israël en ces termes: Établissez-vous des Villes de Refuge, comme je vous l'ai dit par l'organe de Moïse,
“Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
3 qui servent d'asile à l'homicide qui aura tué une personne par mégarde, sans intention; et qu'elles soient pour vous un refuge contre le vengeur du sang.
domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
4 Et qu'il se réfugie dans l'une de ces villes-là, et qu'il se présente à l'entrée de la Porte de la ville et qu'il expose son cas aux oreilles des Anciens de cette ville-là; et ils le recueilleront vers eux dans la ville et lui accorderont un domicile pour y demeurer dans son enceinte avec eux.
Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
5 Et, si le vengeur du sang le poursuit, on ne livrera pas l'homicide entre ses mains, car c'est sans intention qu'il a tué son prochain, et il ne le haïssait ni d'hier, ni d'avant-hier.
In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
6 Et il restera dans cette même ville jusqu'à ce qu'il ait comparu devant l'Assemblée pour être jugé, jusqu'à la mort du Grand-Prêtre qui existera dans ce temps-là. Alors l'homicide pourra s'en retourner et rentrer dans sa ville et dans sa maison, dans la ville d'où il s'était enfui.
Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
7 Et ils consacrèrent Kédès en Galilée dans la montagne de Nephthali et Sichem dans la montagne d'Ephraïm et Kiriath-Arba, c'est-à-dire, Hébron dans la montagne de Juda.
Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
8 Et au delà du Jourdain vers Jéricho à l'orient ils désignèrent Betser dans le désert dans la plaine, de la Tribu de Ruben, et Ramoth en Galaad, de la Tribu de Gad, et Golan en Basan, de la Tribu de Manassé.
A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
9 Telles furent les villes assignées à tous les enfants d'Israël et à l'étranger en séjour chez eux, pour servir d'asile à quiconque tuerait une personne par mégarde, afin qu'il ne meure pas de la main du vengeur du sang, jusqu'à ce qu'il ait comparu devant l'Assemblée.
In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.