< Joël 1 >

1 La parole de l'Éternel qui fut adressée à Joël, fils de Péthuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Entendez-le, vieillards, et prêtez l'oreille, vous tous habitants du pays! Arriva-t-il rien de pareil en vos jours, ou aux jours de vos pères?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Faites-en le récit à vos enfants, et vos enfants à leurs enfants, et leurs enfants à l'âge qui suivra!
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 Ce qu'a laissé le bruche, la locuste le dévore, et ce qu'a laissé la locuste, l'attelabe le dévore, et ce qu'a laissé l'attelabe, la sauterelle le dévore.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Réveillez-vous, vous qui êtes dans l'ivresse, et pleurez! et vous tous, buveurs de vin, gémissez sur le moût, de ce qu'il vous est ôté de la bouche!
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Car un peuple envahit mon pays, puissant et innombrable; ses dents sont des dents de lion, et il a la denture de la lionne;
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 il ravage ma vigne et ronge mon figuier; il l'écorce et en jonche la terre; ses jets restent blancs.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Gémis, [terre!] comme la vierge qui revêt le cilice pour l'époux de sa jeunesse!
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Offrandes et libations sont ôtées à la maison de l'Éternel; les sacrificateurs, ministres de l'Éternel, sont dans le deuil.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Les campagnes sont dévastées, le pays est en deuil, car les blés sont dévastés, la vigne séchée, l'olivier flétri.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Les laboureurs sont confus, et les vignerons gémissent, à cause du froment et de l'orge, parce que la moisson des champs a péri.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 La vigne est séchée et le figuier flétri; le grenadier, le palmier et le pommier aussi, tous les arbres de la campagne ont séché; oui, la joie est tarie pour les enfants d'Adam.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Ceignez [le cilice] et gémissez, ô prêtres! lamentez-vous, ministres de l'autel! Venez, passez la nuit sous le cilice, ministres de mon Dieu! Car les offrandes et les libations sont retranchées à la maison de votre Dieu.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Consacrez un jeûne! convoquez l'assemblée! réunissez les anciens, tous les habitants du pays dans la maison de l'Éternel votre Dieu, et criez à l'Éternel!
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Jour funeste! car le jour de l'Éternel est proche, et comme un ravage de par le Tout-Puissant il arrive.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 Sous nos yeux les subsistances ne sont-elles pas enlevées? de la maison de notre Dieu la joie et l'allégresse n'ont-elles pas disparu?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Les grains semés pourrissent sous leurs glèbes, les magasins sont déserts et les greniers détruits, car les blés ont séché.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Comme le bétail soupire! les troupeaux de bœufs sont angoissés, car ils n'ont point de pâturages; même les troupeaux de brebis en pâtissent.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Éternel, je t'invoque, car un feu dévore les pacages de la plaine, et une flamme brûle tous les arbres des campagnes;
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 les bêtes des champs aussi languissent après toi, car l'eau des ruisseaux est tarie, et un feu dévore les pacages de la plaine.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joël 1 >