< Job 37 >
1 Oui, à ce bruit mon cœur s'épouvante, il s'ébranle et se déplace.
“Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
2 Ecoutez! écoutez le roulement de sa voix, et le murmure qui sort de sa bouche!
Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
3 Il lui fait parcourir tout le ciel, et Il lance l'éclair jusqu'à l'horizon de la terre.
Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
4 Aussitôt sa voix mugit, Il tonne de sa voix de majesté, et ne retient plus sa foudre,
Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
5 Dieu par sa voix produit la merveille du tonnerre; Il fait des choses grandes que nous ne comprenons point.
Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
6 Il dit à la neige: Tombe sur la terre! la pluie et les torrents de pluie attestent sa puissance.
Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
7 Il engourdit les mains de tous les hommes, afin que tous les humains qui sont ses créatures, reconnaissent ce qu'il est.
Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
8 Alors les bêtes sauvages gagnent leurs tanières, et sommeillent dans leurs cavernes.
Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
9 La tempête sort de sa prison, et les vents impétueux amènent la froidure.
Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
10 Au souffle de Dieu la glace est formée, et les ondes dilatées se condensent;
Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
11 d'humidité Il charge aussi la nue; Il épand les nuages porteurs de ses feux,
Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
12 qui tournoient en tout sens, sous sa conduite, pour exécuter tout ce qu'il leur commande, sur la surface du disque de la terre;
Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
13 tantôt pour punir, si sa terre est coupable, tantôt pour bénir, Il les fait arriver.
Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
14 O Job, prête l'oreille à ces choses! continue à étudier les miracles de Dieu!
“Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
15 En sais-tu les causes, quand Dieu les fait paraître, et qu'il fait resplendir le feu de sa nuée?
Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
16 Comprends-tu le balancement des nues, merveille du Dieu parfaitement sage,
Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
17 la chaleur que prennent tes vêtements, quand la terre reçoit du midi un air qui accable?
Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
18 Etendras-tu, comme Lui, le firmament, lui donnant la solidité d'un miroir de fonte?
ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
19 Apprends-nous ce qu'il nous faut Lui dire? Ah! les ténèbres où nous sommes, nous mettent hors d'état de Lui rien proposer!…
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
20 Mes discours lui seront-ils rapportés?… Mais désira-t-on jamais d'être anéanti?
Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
21 Aussi bien l'on ne regarde point fixement le soleil, quand il brille dans les airs, et qu'un vent passe, et lui rend sa pureté.
Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
22 Du Septentrion l'on peut bien tirer l'or, mais Dieu oppose un éclat formidable.
Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
23 Jusqu'au Tout-puissant nous ne saurions pénétrer! Il est éminent par la force et par l'équité, et par une souveraine justice; Il ne rend aucun compte.
Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
24 Craignez-le donc, ô hommes; Il n'accorde ses regards à aucun des sages.
Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”