< Job 21 >

1 Et Job répondit et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Ecoutez, écoutez mon discours, et donnez-moi cette consolation-là!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Souffrez que je parle, et, quand j'aurai parlé, tu pourras te moquer!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Est-ce à l'homme qu'en veut ma plainte? Et pourquoi la patience ne m'échapperait-elle pas?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Tournez les yeux vers moi, et vous serez stupéfaits, et vous mettrez la main sur la bouche!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Quand j'y pense, je me trouble, et ma chair frissonne.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Pourquoi les impies vivent-ils, avancent-ils en âge, accroissent-ils leurs moyens?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Devant eux, autour d'eux, leur race s'affermit, et leurs rejetons réjouissent leurs regards.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Leurs maisons sont en paix, à l'abri de la crainte, et la verge de Dieu ne passe point sur eux.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Leur taureau saillit, et n'est point impuissant, leur génisse vêle, et n'avorte point.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 Ils promènent leur famille qui égale un troupeau, et leurs enfants s'ébattent.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 Ils chantent au son des cymbales et du luth, et s'égaient au bruit de la cornemuse.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 Ils emploient leurs jours à jouir, et la descente aux Enfers est pour eux l'affaire d'un instant. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Cependant ils disent à Dieu: « Retire-toi de nous! et pour la science de tes voies nous n'avons aucun goût.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Qu'est-ce que le Tout-puissant, pour que nous le servions? et que gagnerions-nous à le prier? »
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Voici, n'ont-ils pas leur bonheur en leurs mains? (Loin de moi les principes des impies!)
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Combien de fois arrive-t-il que la lampe des impies s'éteigne, et que leur ruine fonde sur eux; que Dieu leur distribue leurs lots dans sa colère;
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 qu'ils soient comme le chaume au souffle du vent, ou comme la balle qu'enlève l'ouragan?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 C'est à ses fils que Dieu réserve la misère! C'est lui que Dieu devrait punir, afin qu'il en pâtit;
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 c'est lui qui de ses yeux devrait contempler sa chute, et être abreuvé du courroux du Tout-puissant!
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Car, que lui fait sa maison après lui, quand le terme de ses jours est échu?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Est-ce à Dieu qu'on veut révéler la science, à lui qui juge les Intelligences célestes?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 L'un meurt au sein même du bien-être, dans une sécurité et une paix complète;
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 ses bergeries sont remplies de lait, et la moelle de ses os est toujours rafraîchie.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Et l'autre meurt, l'amertume dans l'âme, et il n'a point goûté le bonheur.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 Ensemble ils sont gisants dans la poudre, et les vers les recouvrent.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Voici, je sais quelles sont vos pensées, et les jugements qu'à tort vous portez sur moi!
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 Car vous dites: « Où est la maison de l'homme puissant, et la tente où habitaient les impies? »
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 N'avez-vous pas interrogé les voyageurs? et ne vous rendrez-vous pas aux preuves qu'ils rapportent?
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 C'est qu'au jour de la ruine, l'impie est préservé, et qu'au jour des vengeances, il est conduit en lieu sûr.
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 Qui est-ce qui lui reproche en face sa conduite, et qui est-ce qui lui rend ce qu'il a fait?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Il est porté au tombeau, et il veille encore sur le tertre.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 La terre de la vallée pèse doucement sur lui; après lui tous les hommes vont à la file, et ses devanciers sont innombrables.
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Comment pouvez-vous donc m'offrir des consolations si vaines? De vos réponses, ce qui reste, c'est la perfidie.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >