< Job 20 >
1 Et Zophar de Naama répondit et dit:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Mes pensées vont, et pour cause, me fournir la réplique; aussi j'ai hâte de la faire:
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 j'ai dû entendre une leçon qui m'outrage! mais l'esprit selon mes lumières répondra pour moi.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Ne sais-tu pas que, de tout temps, depuis que l'homme fut placé sur la terre,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 la joie des impies est de courte durée, et l'allégresse des profanes n'a qu'un instant?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Que sa grandeur s'élève jusques aux Cieux, et que sa tête touche aux nues,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 pour toujours il périt comme les excréments; ceux qui l'ont vu, demandent: Où est-il?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Il s'envole comme un songe, et on ne le retrouve pas; il a fui comme une vision nocturne;
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 l'œil qui l'a vu, ne l'aperçoit plus, et sa demeure ne le reverra pas.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Les indigents accablent ses fils dont les mains doivent restituer ses biens,
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Ses os surabondaient d'une vigueur juvénile, et sur la poussière elle gît avec lui.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Quelque douceur que sa bouche trouve au mal, qu'il le tienne en réserve sous sa langue,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 le savourant lentement, sans le laisser aller, mais le retenant collé à son palais,
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 cet aliment qu'il prend, se transforme dans ses entrailles, et devient au dedans de lui un venin d'aspic,
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Il engloutit des richesses, et il les revomit; de son ventre Dieu les fait ressortir,
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 il suce le venin de l'aspic, et la langue de la vipère le tue.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Son regard n'est plus réjoui par les ruisseaux, ni par les fleuves, les torrents de miel et de lait.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Il restitue ses gains, et ne les consomme pas: autant il possède, autant il restitue, et il ne peut se réjouir.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Car il écrasa, délaissa les pauvres, il ravit des maisons, et ne les releva pas;
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 car il ne connut pas le repos dans son sein. Mais il ne se sauvera pas avec ce qu'il a de plus cher,
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Rien n'échappe à sa voracité, c'est pourquoi son bien-être ne dure pas.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Dans la plénitude de l'abondance, il est mis à la gêne; les bras des opprimés fondent sur lui.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 Voici Celui qui assouvira son avidité: Il enverra sur lui le feu de Sa colère, et fera pleuvoir sur lui Son pain de douleur;
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 s'il fuit devant l'armure de fer, l'arc d'airain le transperce.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Il extrait le dard de son corps avec le fer brillant qui lui a percé le foie; c'en est fait: il est sous les terreurs de la mort.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Toutes les misères lui sont réservées en échange de ce qu'il a mis en réserve; un feu qu'on n'a pas à souffler, le dévore, et consume ce qui resterait dans sa tente.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Le ciel dévoile son crime, et la terre s'élève contre lui.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Tout le revenu de sa maison s'en va, s'écoulant au jour de Sa colère.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Telle est la part que Dieu donne à l'impie, et le lot que le Seigneur lui décerne.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”