< Jérémie 46 >
1 La parole de l'Éternel qui fut adressée à Jérémie, le prophète, touchant les nations.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Sur l'Egypte, sur l'armée de Pharaon Néco, roi d'Egypte, qui était près du fleuve de l'Euphrate à Carchémis, et que battit Nébucadnézar, roi de Babel, la quatrième année de Jéhojakim, fils de Josias, roi de Juda.
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 Apprêtez le bouclier et le pavois, et marchez au combat!
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Attelez les chevaux! et montez-y, cavaliers! prenez vos rangs avec vos casques! nettoyez les lances! endossez la cuirasse!
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 Pourquoi les vois-je reculer épouvantés? Leurs héros sont battus, ils fuient sans tourner la tête: terreur de toute part! dit l'Éternel.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 Point de fuite pour les agiles, point de salut pour les forts; au nord, près de l'Euphrate, ils trébuchent et tombent.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 Qui est celui qui s'avance pareil au Nil? comme les torrents ses eaux se meuvent!
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 L'Égyptien s'avance pareil au Nil, et comme les torrents ses eaux se meuvent, et il dit: Je m'avance, je vais couvrir le pays, ruiner des villes et leurs habitants!
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Coursiers, en avant! chars, roulez avec furie! et que les guerriers paraissent, Éthiopiens et Libyens portant le bouclier, et Lydiens portant et bandant les arcs!
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 Cette journée est au Seigneur, à l'Éternel des armées, c'est une journée de vengeance pour Le venger de ses ennemis; et l'épée dévore et s'assouvit, et s'enivre de leur sang, car il se fait un sacrifice au Seigneur, à l'Éternel des armées, dans le pays du nord près de l'Euphrate.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Monte à Galaad, et y prends du baume, Vierge, fille de l'Egypte! En vain multiplies-tu les remèdes; pour toi il n'y a point de pansement.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 Les nations entendent parler de ton opprobre, et la terre se remplit de tes cris, car le guerrier sur le guerrier trébuche, et ensemble ils tombent tous les deux.
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 La parole qu'adressa l'Éternel à Jérémie, le prophète, sur ce que Nébucadnézar, roi de Babel, viendrait pour frapper le pays d'Egypte.
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 Publiez en Egypte, et proclamez à Migdol, et proclamez à Noph, et à Tachphanès! dites: Debout! équipe-toi, car l'épée sévit autour de toi!
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Pourquoi tes chefs sont-ils terrassés? Ils n'ont pas tenu tête; car l'Éternel les a renversés;
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 en foule ils trébuchent et tombent l'un sur l'autre, et disent: Levez-vous, et retournons dans notre peuple, et au pays de notre naissance, fuyant la cruelle épée!
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 Là on s'écrie: Pharaon, roi d'Egypte, est perdu! il a laissé passer le moment.
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 Par ma vie, dit le Roi dont l'Éternel des armées est le nom, semblable au Thabor entre les montagnes, et semblable au Carmel au-dessus de la mer, il arrive.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 Prépare-toi pour la captivité, toi qui habites en ces lieux, fille de l'Egypte; car Noph sera saccagée et brûlée, dépeuplée.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 L'Egypte est une génisse superbe; un aiguillon vient du nord, il arrive.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Même les mercenaires qui sont au milieu d'elle, tels que des veaux engraissés, oui, eux aussi, ils tournent le dos; ils fuient de concert, ils ne s'arrêtent pas, car sur eux fond le jour de leur supplice, le temps de leur châtiment.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 Sa voix sortira perçante comme celle du serpent, quand en force ils arriveront, et qu'ils marcheront sur elle armés de haches, pareils à des bûcherons.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 Ils vont couper sa forêt, dit l'Éternel, car elle est impénétrable, car ils sont plus nombreux que des sauterelles, et on ne peut les compter.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 La fille de l'Egypte est honteuse; elle est livrée aux mains d'un peuple du septentrion.
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 L'Éternel des armées, Dieu d'Israël, a dit: Voici, je vais châtier Amon de No, et Pharaon, et l'Egypte, et ses dieux et ses rois, Pharaon et ceux qui s'appuient sur lui,
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 et les livrer aux mains de ceux qui en veulent à leur vie, et aux mains de Nébucadnézar, roi de Babel, et aux mains de ses serviteurs; mais dans la suite [l'Egypte] sera habitée comme aux jours d'autrefois, dit l'Éternel.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 Pour toi, ne crains point, ô mon serviteur Jacob! et ne t'effraie point, Israël! car voici, je te retirerai des pays lointains, et ta race de la contrée où elle est prisonnière; et Jacob reviendra, et il sera tranquille et heureux, sans alarmes.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 Toi, ô mon serviteur Jacob, sois sans peur, dit l'Éternel! car je suis avec toi! quand j'exterminerai toutes les nations où je t'ai disséminé, toi, je ne t'exterminerai point; et je te châtierai, mais avec mesure; car je ne puis te laisser impuni.
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”