< Jérémie 27 >
1 Au commencement du règne de Jéhojakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole fut adressée à Jérémie par l'Éternel, disant:
A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Ainsi m'a parlé l'Éternel: Fais-toi des chaînes et des jougs, et mets-les à ton col;
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
3 puis envoie-les au roi d'Édom, et au roi de Moab, et au roi des fils d'Ammon, et au roi de Tyr, et au roi de Sidon, par l'intermédiaire des députés venus à Jérusalem auprès de Sédécias, roi de Juda;
Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
4 et donne-leur mes ordres pour leurs maîtres en ces termes: Ainsi parle l'Éternel des armées, Dieu d'Israël: Ainsi parlerez-vous à vos maîtres:
Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
5 C'est moi qui ai fait la terre, et l'homme et les animaux qui sont sur la terre, par ma grande puissance et par mon bras étendu, et je les donne à qui bon me semble;
Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
6 et maintenant je remets tous ces pays entre les mains de Nébucadnézar, roi de Babel, mon serviteur; et je lui donne aussi les bêtes des champs pour lui être assujetties,
Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
7 et tous les peuples lui seront assujettis, à lui et à son fils, et au fils de son fils, jusqu'à ce que le temps de son pays arrive aussi, et que des peuples nombreux et de grands rois l'asservissent.
Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
8 Et le peuple et le royaume qui ne se soumettra pas à lui, à Nébucadnézar, roi de Babel, et celui qui ne présentera pas son col au joug du roi de Babel, ce peuple-là, je le châtierai de l'épée, et de la famine, et de la peste, dit l'Éternel, jusqu'à ce que je l'aie exterminé par sa main.
“‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
9 Et vous, n'écoutez pas vos prophètes, ni vos devins, ni vos songes, ni vos magiciens, ni vos enchanteurs qui en vous parlant vous disent: Vous ne serez pas asservis au roi de Babel;
Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
10 car c'est le mensonge qu'ils vous prophétisent, afin de vous bannir de votre pays, et afin que je vous chasse et que vous périssiez.
Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
11 Mais le peuple qui passera son col dans le joug du roi de Babel, et se soumettra à lui, je le laisserai sur son sol, dit l'Éternel, pour qu'il le cultive et y demeure.
Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
12 Et je parlai à Sédécias, roi de Juda, en ces mêmes termes, disant: Passez vos cols dans le joug du roi de Babel, et soumettez-vous à lui et à son peuple, afin que vous viviez.
Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
13 Pourquoi voudriez-vous, toi et ton peuple, mourir par l'épée, la famine et la peste, comme l'Éternel en a menacé le peuple qui ne se soumettra pas au roi de Babel?
Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
14 Et n'écoutez pas les discours des prophètes qui vous disent: Vous ne serez pas asservis au roi de Babel; car c'est le mensonge qu'ils vous prophétisent.
Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
15 Car je ne les ai pas envoyés, dit l'Éternel, et ils prophétisent en mon nom le mensonge, pour que je vous chasse, et que vous périssiez, vous et les prophètes qui vous prophétisent.
‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
16 Et je parlai aux sacrificateurs et à tout ce peuple, disant: Ainsi parle l'Éternel: N'écoutez pas les discours de vos prophètes qui vous prophétisent disant: Voici, maintenant les meubles de la maison de l'Éternel seront bientôt rapportés de Babel! car c'est un mensonge qu'ils vous prophétisent.
Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
17 Ne les écoutez pas, soumettez-vous au roi de Babel, et vous vivrez; pourquoi cette ville serait-elle dévastée?
Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
18 Que s'ils sont des prophètes, et si la parole de l'Éternel est avec eux, qu'ils demandent à l'Éternel des armées, que les meubles restés dans la maison de l'Éternel, et dans la maison du roi de Juda, et à Jérusalem, n'aillent point à Babel;
In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
19 car ainsi prononce l'Éternel des armées sur les colonnes, et sur la mer, et sur les piédestaux, et sur les meubles restés dans cette ville,
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
20 que n'a point enlevés Nébucadnézar, roi de Babel, en emmenant captifs de Jérusalem à Babel Jéchonias, fils de Jéhojakim, roi de Juda, et tous les Grands de Juda et de Jérusalem –
waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
21 car ainsi prononce l'Éternel des armées, Dieu d'Israël, sur les meubles qui restent dans la maison de l'Éternel, et dans la maison du roi de Juda et à Jérusalem:
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
22 ils iront à Babel, et y demeureront, jusqu'au jour où je m'aviserai d'eux, dit l'Éternel, et où je les ferai remonter et revenir en ce lieu-ci.
‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”