< Jérémie 11 >

1 La parole qui fut adressée à Jérémie de par l'Éternel en ces mots:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 Écoutez les paroles de cette alliance, et dites-les aux hommes de Juda et aux habitants de Jérusalem!
“Ka saurari zancen wannan alkawari ka kuma faɗe su ga mutanen Yahuda da kuma waɗanda suke zaune a Urushalima.
3 Et tu leur diras: Ainsi parle l'Éternel, Dieu d'Israël: Maudit l'homme qui n'écoute pas les paroles de cette alliance,
Ka faɗa musu cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa, ‘La’ananne ne wanda bai kula da zancen alkawarin nan ba,
4 que je prescrivis à vos pères le jour où je les tirai du pays d'Egypte, du fourneau de fer, en disant: Obéissez à ma voix, et faites tout ce que je vous commanderai, et vous serez mon peuple, et je serai votre Dieu,
zancen da na umarci kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga cikin tanderun narkewar ƙarfe.’ Na ce, ‘Ku yi mini biyayya ku kuma aikata kowane abin da na umarce ku, za ku kuwa zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
5 pour que j'accomplisse le serment que je fis à vos pères, de leur donner le pays découlant de lait et de miel, comme [vous le voyez] aujourd'hui. Et je répondis et dis: Ainsi soit-il, Éternel!
Sa’an nan zan cika rantsuwar da na yi wa kakanni-kakanninku, da zan ba su ƙasa mai zub da madara da kuma zuma’ ƙasar da kuka mallaka a yau.” Sai na amsa na ce, “Amin, Ubangiji.”
6 Et l'Éternel me dit: Proclame toutes ces paroles dans les villes de Juda et dans les rues de Jérusalem, disant: Écoutez les paroles de cette alliance, et exécutez-les.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuda da titunan Urushalima duka cewa, ‘Su saurari zancen alkawarin nan, su aikata.
7 Car je sommai vos pères dès le jour où je les tirai du pays d'Egypte, jusqu'aujourd'hui, les sommant dès le matin et disant: Obéissez à ma voix!
Daga lokacin da na fitar da kakanni-kakanninku daga Masar har yă zuwa yau, na gargaɗe su sau da sau, ina cewa, “Ku yi mini biyayya.”
8 Mais ils n'ont ni obéi, ni prêté l'oreille, et ils ont marché chacun suivant l'obstination de son cœur mauvais; aussi j'exécuterai sur eux toutes les paroles de cette alliance que je leur commandai d'observer, et qu'ils n'ont point observée.
Amma ba su kasa kunne ko su saurara ba, a maimako, sai suka bi taurinkai na mugayen zukatansu. Saboda haka na kawo musu dukan la’anonin alkawarin da na riga na umarce su, su bi amma ba su kiyaye ba.’”
9 Et l'Éternel me dit: Il existe une conjuration entre les hommes de Juda et les habitants de Jérusalem.
Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, “Akwai maƙarƙashiya a cikin mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima.
10 Ils retournent aux péchés de leurs premiers pères qui refusèrent d'obéir à mes paroles, et suivirent d'autres dieux pour les servir: la maison d'Israël et la maison de Juda ont rompu l'alliance que j'avais traitée avec leurs pères.
Sun koma ga zunuban kakanni kakanninsu, waɗanda suka ƙi su saurari maganata. Suka bi waɗansu alloli don su bauta musu. Da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda duk sun take alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu.
11 Aussi, ainsi parle l'Éternel: Voici, j'amène sur vous des maux d'où vous ne pourrez sortir; et ils crieront vers moi, mais je ne les écouterai pas.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan kawo masifa a kansu wadda ba za su iya tsere mata ba. Ko da yake suna kuka gare ni, ba zan saurare su ba.
12 Qu'elles aillent donc, les villes de Juda, et les habitants de Jérusalem! et qu'ils crient aux dieux qu'ils encensent; mais ils ne leur aideront point au moment de leur malheur.
Garuruwan Yahuda da mutanen Urushalima za su tafi su yi kuka ga allolin da suke ƙona wa turare, amma ba za su taimake su ba sam sa’ad da masifar ta auku.
13 Car tel le nombre de tes villes, tel est le nombre de tes dieux, Juda, et autant il y a de rues à Jérusalem, autant vous avez élevé d'autels à l'infamie, d'autels pour encenser Baal.
Kuna da alloli masu yawa yadda kuke da garuruwa, ya Yahuda; kuma bagadan da kuka yi don ƙona turare wa allahn nan Ba’al abin kunya sun yi yawa kamar titunan Urushalima.’
14 Mais toi, n'intercède pas pour ce peuple, et en sa faveur n'élève ni supplication, ni prière, car je n'écouterai point quand ils m'invoqueront à cause de leurs maux.
“Kada ka yi addu’a domin wannan mutane ko ka miƙa wani roƙo ko kuka dominsu, domin ba zan saurara ba sa’ad da suka kira gare ni a lokacin ƙuncinsu.
15 Qu'y a-t-il pour mon bien-aimé dans ma maison? La foule y fait le crime. La chair sacrée te laissera à découvert, quand tes maux arriveront; c'est alors que tu seras alarmé.
“Mene ne ƙaunatacciyata take yi a haikali da yake ta yin ƙulle-ƙullen mugayen makircinta tare da mutane masu yawa? Tsarkakar nama zai iya kawar da hukuncinki? Sa’ad da kike yin muguntarki sa’an nan ki yi farin ciki.”
16 Olivier verdoyant, beau de son fruit aimable, tel est le nom que tu reçus de l'Éternel. Au bruit d'un grand fracas Il allume le feu autour de lui, et l'on brise ses rameaux;
Ubangiji ya kira ki itacen zaitun mai inuwa kyakkyawa mai’ya’ya masu kyau. Amma da ƙugin babbar hadari zai cinna masa wuta, rassansa za su kakkarye.
17 et l'Éternel des armées qui te planta, t'annonce des calamités à cause de la méchanceté qu'ont montrée la maison d'Israël et la maison de Juda, pour m'irriter en encensant Baal.
Ubangiji Maɗaukaki, wanda ya dasa ki, ya furta miki masifa, domin gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda sun aikata mugunta suka kuma tsokane ni in yi fushi ta wurin ƙona wa Ba’al turare.
18 L'Éternel m'a informé, et j'ai su…, c'est alors que Tu as mis pour moi leurs œuvres en évidence.
Domin Ubangiji ya bayyana mini maƙarƙashiyarsu, na santa, gama a wannan lokaci ya nuna mini abin da suke yi.
19 Cependant j'étais comme l'agneau familier que l'on mène à la tuerie, et je ne me doutais pas qu'ils méditassent des plans contre moi: « Détruisons l'arbre avec son fruit, et extirpons-le de la terre des vivants, et que son nom ne soit plus rappelé! »
Na kasance kamar ɗan rago marar faɗa wanda aka kai mayanka; ban gane cewa sun ƙulla mini maƙarƙashiya, suna cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da’ya’yansa; bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”
20 Mais l'Éternel des armées est un juste Juge; Il sonde les reins et le cœur. Je serai témoin de la vengeance que tu tireras d'eux, car c'est à Toi que je me suis ouvert de mes griefs.
Amma, ya Ubangiji Maɗaukaki, kai da kake yin shari’a da adalci kake gwada zuciya da kuma tunani, ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, gama a gare ka na danƙa maganata.
21 Aussi, voici ce que prononce l'Éternel contre les gens d'Anathoth qui en veulent à ma vie et disent: « Ne prophétise plus au nom de l'Éternel, si tu veux ne pas mourir de notre main! »
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka suna kuma cewa, ‘Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji in ba haka za ka mutu a hannunmu’
22 Aussi, voici ce que l'Éternel des armées prononce: Voici, je vais les châtier: les jeunes hommes périront par l'épée, et leurs fils et leurs filles périront par la famine;
saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘Zan hukunta su. Samarinsu za su mutu ta wurin takobi,’ya’yansu maza da mata kuwa ta wurin yunwa.
23 et rien ne restera d'eux; car je vais amener des maux sur les hommes d'Anathoth, au temps de leur châtiment.
Babu raguwar da za a bar musu, domin zan kawo masifa a kan mutanen Anatot a shekarar hukuncinsu.’”

< Jérémie 11 >