< Isaïe 9 >
1 Mais il ne fera pas [toujours] sombre là où il y a [maintenant] angoisse. Si les premiers temps ont couvert d'opprobre le pays de Zabulon et le pays de Nephthali, les temps qui suivront couvriront de gloire la côte de la mer, au-delà du Jourdain, la contrée des Gentils.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 Le peuple qui marche dans les ténèbres, voit une grande lumière: sur ceux qui sont assis au pays de l'ombre de mort, resplendit une lumière.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Tu rends le peuple nombreux, tu augmentes sa joie; ils se réjouissent devant toi, comme on se réjouit à la moisson, comme on s'égaie au partage du butin.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 Car le joug qui lui pèse, la verge qui bat son épaule, et le bâton de son oppresseur, tu le brises comme à la journée de Madian.
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 Car toute chaussure qu'on chausse dans la mêlée, et tout habit de guerre roulé dans le sang, seront brûlés, seront la proie des flammes.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 Car un enfant nous est né, un Fils nous est donné, et l'empire repose sur son épaule, et on lui donne pour nom Merveille, Conseiller, Dieu Fort, Père éternel, Prince de paix,
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 pour l'accroissement de l'empire, et pour une paix sans fin sur le trône de David et sur son royaume, afin de l'affermir et de le soutenir par le droit et la justice, dès maintenant à l'éternité. C'est ce qu'opérera le zèle de l'Éternel des armées.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 Le Seigneur dirige contre Jacob une parole, qui va frapper Israël,
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 et elle se fera sentir à tout le peuple, à Éphraïm et aux habitants de Samarie qui, dans l'orgueil et la fierté du cœur, disent:
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 « Des briques se sont écroulées, et en pierres de taille nous rebâtirons; des sycomores ont été coupés, et par des cèdres nous les remplacerons. »
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Car l'Éternel rendra les ennemis de Retsin supérieurs à eux, et Il armera leurs ennemis,
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 les Syriens par devant et les Philistins par derrière, pour qu'ils mangent Israël à pleine bouche. Malgré tout cela, sa colère ne cesse point, et sa droite est encore étendue.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 Mais le peuple ne revient pas à Celui qui le frappe, et de l'Éternel des armées ils ne s'enquièrent pas.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Aussi l'Éternel arrachera d'Israël la tête et la queue, le rameau de palmier et le jonc, en un même jour.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 (L'ancien et le noble, c'est la tête; et le prophète docteur de mensonge, c'est la queue.)
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 Car les guides de ce peuple l'égarent, et ceux qui se laissent guider se perdent.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 C'est pourquoi le Seigneur n'aura point de joie à voir ses jeunes hommes, et de ses orphelins et de ses veuves; Il n'aura point de pitié, car tous ils sont sacrilèges et méchants, et toutes les bouches parlent follement. Malgré tout cela, sa colère ne cesse point, et sa main est encore étendue.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 Car la méchanceté brûle comme un feu qui dévore les ronces et les épines, et embrase le fort de la forêt, et s'élève en colonnes de fumée.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 Par la colère de l'Éternel des armées le pays est incendié, et le peuple devient la proie des flammes; nul n'épargne son frère.
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 On dévore à droite, et l'on est affamé; on mange à gauche, et l'on n'est pas rassasié: chacun mange la chair de ses proches.
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 Manassé [dévore] Éphraïm, et Éphraïm Manassé, et les deux ensemble fondent sur Juda. Malgré tout cela, sa colère ne cesse pas, et sa main est toujours étendue.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.