< Isaïe 57 >
1 Le juste périt et nul n'y prend garde, et les gens de bien sont enlevés, sans que nul remarque que le juste est enlevé par l'effet de la malice.
Mai adalci yakan mutu, ba kuwa wanda yakan yi tunani a zuciyarsa; an kwashe mutanen kirki, ba kuwa wanda ya fahimta cewa an kwashe masu adalci don a tsame su daga mugunta.
2 Il entre dans la paix; ils reposent sur leur couche, ceux qui marchent droit.
Waɗanda suke aikata abin da yake daidai sukan shiga da salama; sukan huta yayinda suka kwanta cikin kabari.
3 Mais vous, avancez ici, fils d'enchanteresse, race de l'adultère et de la prostituée!
“Amma ku, ku matso nan, ku’ya’ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinata da karuwai!
4 Aux dépens de qui vous égayez-vous? A qui présentez-vous une bouche élargie, tirez-vous la langue? N'êtes-vous pas des enfants de la révolte, une race menteuse,
Wane ne kuke yi wa ba’a? Ga wa kuke masa gwalo kuna kuma fitar da harshe? Ashe, ku ba tarin’yan tawaye ba ne, zuriyar maƙaryata?
5 brûlant pour des idoles sous tout arbre vert, immolant des enfants dans les vallées, dans les creux des rochers?
Kuna cike da muguwar sha’awa mai ƙonawa a cikin itatuwan oak da kuma a ƙarƙashin kowane itace mai inuwa; kuna miƙa hadayar’ya’yanku a rafuffuka da kuma a ƙarƙashin tsagaggun duwatsu.
6 Les pierres des torrents sont ton partage, c'est elles qui sont ton lot; à elles aussi tu fais des libations, tu présentes des oblations: y puis-je être insensible?
Gumakan da suke cikin duwatsu masu sulɓi su ne rabonku; su ɗin, su ne rabonku. I, gare su kuka kwarara hadayu na sha kuka kuma miƙa hadayu na gari. Saboda waɗannan abubuwa, zan yi haƙuri?
7 Sur une montagne haute et éminente tu dresses ton lit, et l'a aussi tu montes pour offrir des victimes.
Kun yi gadonku a dogayen duwatsu masu tsayi da kuma a tudu mai tsawo; a can kuka haura don ku miƙa hadayunku.
8 Et derrière la porte et les jambages tu places les objets de ta pensée. Car me désertant, tu découvres ton lit et y montes, et tu l'as rendu spacieux, et tu leur fais tes conditions, et tu aimes leur commerce: tu te choisis une place.
A bayan ƙofofi da madogaran ƙofofi kuka kafa alamun gumakanku. Kuka yashe ni, kuka kware gadonku, kuka kwanta a kansa kuka fadada shi; kuka kuma ƙulla yarjejjeniya da waɗanda kuke ƙaunar gadajensu, kuka dubi tsiraicinsu.
9 Et tu te présentes au roi avec de l'huile, ayant sur toi beaucoup de parfums; tu envoies tes messagers au loin, et les fais pénétrer jusqu'aux Enfers. (Sheol )
Kuka tafi wurin Molek da man zaitun kuka kuma riɓaɓɓanya turarenku. Kuka aika jakadunku can da nisa; kuka gangara zuwa cikin kabari kansa! (Sheol )
10 A force de voyager tu te fatigues, mais tu ne dis pas: C'est en vain! Tu trouves encore de la vigueur en ta main; aussi n'es-tu pas affaiblie!
Kuka gaji cikin dukan al’amuranku, amma ba ku iya cewa, ‘Aikin banza ne ba.’ Kuka sami sabuntar ƙarfinku, ta haka ba ku suma ba.
11 Et qui donc crains-tu et redoutes-tu, que tu dissimules et ne te souviens pas de moi? Tu n'en as pas tenu compte! N'est-ce pas? je garde le silence, et même depuis longtemps; c'est pourquoi tu ne me crains pas!
“Wa ya sa ku fargaba, kuna jin tsoro har kuka yi mini ƙarya, ba ku kuma tuna da ni ba balle ku yi tunanin wannan a zukatanku? Ba don na daɗe ina shiru ba ne ya sa ba kwa tsorona?
12 Je mettrai ta justice au jour, et tes œuvres qui ne te profiteront pas.
Zan bayyana adalcinku da kuma ayyukanku, ba kuwa za su amfane ku ba.
13 Quand tu cries, tes bandes de dieux te sauveront-elles? Eh! un coup de vent les enlève tous, un souffle les emporte. Mais qui se confie en moi, héritera le pays et possédera ma montagne sainte;
Sa’ad da kuka nemi taimako, bari tarin gumakanku su cece ku! Iska za tă kwashe dukansu tă tafi, ɗan numfashi kawai zai hura su. Amma mutumin da ya mai da ni mafakarsa zai gāji ƙasar ya kuma mallaki dutsena mai tsarki.”
14 et il dit: Frayez, frayez, préparez le chemin, ôtez tout achoppement de la route de mon peuple!
Za a kuma ce, “Ku gina, ku gina, ku gyara hanya! Ku kawar da abubuwan sa tuntuɓe a hanyar mutanena.”
15 Car ainsi parle le Suprême, l'Éminent dont le trône est éternel, et qui s'appelle le Saint: J'habite les lieux très hauts et saints, mais aussi près de l'affligé et de l'homme abattu d'esprit, pour ranimer l'esprit des hommes abattus, et ranimer le cœur des affligés.
Gama abin da Maɗaukaki da kuma Mai daraja ya faɗa wanda yake raye har abada, wanda sunansa mai tsarki ne, “Ina zama a bisa da kuma a tsattsarkan wuri, amma kuma tare da shi wanda yake mai halin tuba mai tawali’u a ruhu, don in farfaɗo da ruhu mai tawali’u in kuma farfaɗo da zuciyar mai halin tuba.
16 Car je ne veux pas contester à toujours, ni garder une colère éternelle, puisqu'à ma présence l'esprit et les âmes que j'ai faites, tombent en défaillance.
Ba zan tuhume su har abada ba, ba kuwa kullum zai yi fushi ba, gama a haka ruhun mutumin zan yi suma a gabana, shi numfashin mutumin da na halitta.
17 Pour le crime de son avarice je m'irritai et le frappai, je me cachai, et m'irritai: rebelle néanmoins, il suivit la voie que lui montrait son cœur.
Na yi fushi saboda kwaɗayin zunubinsa; na yi masa horo, na kuma ɓoye fuskata saboda fushi, duk da haka ya ci gaba da ayyukan zunubinsa.
18 J'ai vu ses voies; mais je veux le guérir, et le conduire, et lui donner des consolations à lui et à ses affligés,
Na ga al’amuransa, amma zan warkar da shi; zan bi da shi in mayar da ta’aziyya a gare shi,
19 faisant éclater la louange sur ses lèvres. Paix, paix, pour celui qui est loin, et pour celui qui est près, dit l'Éternel! je veux les guérir.
ina ƙirƙiro yabo a leɓunan masu makoki a Isra’ila. Salama, salama, ga waɗanda suke nesa da kuma kusa,” in ji Ubangiji. “Zan kuma warkar da su.”
20 Mais les impies sont comme la mer agitée; car elle ne peut se calmer, et les eaux soulèvent du limon et de la vase.
Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, wanda ba ya natsuwa, wanda raƙumansa sukan kawo gurɓacewa da tabo.
21 Point de paix, dit mon Dieu, pour les impies!
“Babu salama ga mugaye,” in ji Allahna.