< Isaïe 44 >
1 Mais maintenant, écoute, O Jacob mon serviteur, et Israël dont j'ai fait choix!
“Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.
2 Ainsi parle l'Éternel, ton créateur et ton formateur dès l'origine de ta naissance, ton aide: Ne crains point, Jacob mon serviteur, et mon Israël dont j'ai fait choix!
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi wanda ya yi ka, wanda ya siffanta ka a cikin mahaifa, wanda kuma zai taimake ka. Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub, bawana, Yeshurun, wanda na zaɓa.
3 car je répandrai des eaux sur le sol altéré, et des ruisseaux sur la terre sèche; je répandrai mon esprit sur ta race, et ma bénédiction sur tes rejetons,
Gama zan zuba ruwa a ƙeƙasasshiyar ƙasa, rafuffuka kuma a busasshiyar ƙasa; zan ba da Ruhuna ga’ya’yanka, albarkata kuma ga zuriyarka.
4 afin qu'ils poussent parmi la verdure, comme des saules auprès des courants d'eau.
Za su tsiro kamar ciyawa a wuriyar ruwa, kamar kurmi kusa da rafuffuka masu gudu.
5 L'un dira: « J'appartiens à l'Éternel! » et l'autre se réclamera du nom de Jacob, et un autre mettra sur sa main la marque de l'Éternel, et dira avec amour le nom d'Israël.
Wani zai ce, ‘Ni na Ubangiji ne’; wani kuma zai kira kansa da sunan Yaƙub; har yanzu wani zai rubuta a hannunsa, ‘Na Ubangiji,’ ya kuma ɗauki sunan Isra’ila.
6 Ainsi parle l'Éternel, Roi d'Israël et son Rédempteur, l'Éternel des armées: Je suis le premier et le dernier, et hors moi il n'y a point de Dieu.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Sarki da kuma Mai Fansar Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki. Ni ne farko ni ne kuma ƙarshe; in ban da ni babu wani Allah.
7 Et qui comme moi a fait des prophéties (qu'on le dise et me le mette en avant!) depuis que je fondai le peuple éternel? Et qu'ils annoncent l'avenir et ce qui doit arriver!
Wane ne kuwa kama da ni? Ya faɗa a ji. Bari yă yi shela ya kuma nuna shi a gabana mene ne ya faru tun da na kafa mutanena na dā, mene ne kuma bai riga ya faru ba, I, bari yă faɗa abin da zai zo.
8 Soyez sans crainte et sans peur! dès longtemps ne te l'ai-je pas annoncé et déclaré? aussi bien vous êtes mes témoins! Y a-t-il un Dieu hors moi? Il n'y a point de rocher, je n'en connais aucun.
Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
9 Les faiseurs d'idoles sont tous une vanité et leurs chefs-d'œuvre ne servent à rien, ils sont leurs propres témoins: ils ne voient pas et n'ont pas la connaissance, afin qu'ils soient honteux.
Duk masu yin gumaka ba kome ba ne, da kuma abubuwan da suke ɗauka da daraja banza ne. Waɗanda za su yi magana a madadinsu makafi ne; jahilai ne, marasa kunya.
10 Qui forgerait un Dieu, ou fondrait une image, pour n'en rien retirer?
Waɗanda suke siffanta allah su kuma yi zubin gunki, waɗanda ba za su yi musu ribar kome ba?
11 Voici tous ceux qui y coopèrent, auront à rougir; et les ouvriers ne sont que des hommes: ils sont là réunis, debout, tremblants et confus tous ensemble.
Shi da irinsa za su sha kunya; masu sassaƙa ba kome ba mutane ne kurum. Bari su tattaru su ɗauki matsayinsu; za su firgita su kuma sha mummunan kunya.
12 Le forgeron forge une hache et travaille au feu des charbons, et la façonne avec le marteau, et la travaille à force de bras; il a faim aussi, et n'a plus de forces, il ne boit point d'eau, et il est épuisé.
Maƙeri yakan ɗauki kayan aiki ya yi aiki da shi a cikin garwashi; ya ƙera gunki da guduma, ya gyara shi da hannuwansa masu ƙarfi. Yakan ji yunwa ya kuma rasa ƙarfi; yakan sha ruwa ya kuma ji gajiya.
13 Le charpentier étend un cordeau; et en fait le dessin avec le style, et la façonne avec le rabot, et en fait le tracé avec le compas; il lui donne ainsi une forme humaine, une belle figure d'homme, digne d'habiter un temple.
Kafinta yakan gwada katako yă kuma zāna siffar da alli; yă goge shi da kayan aiki yă kuma zāna shi da alƙalami. Yă siffanta shi a kamannin mutum, mutum cikin dukan darajarsa, don yă ajiye shi a cikin masujada.
14 Il va se couper des cèdres, et prend un rouvre et un chêne, et fait un choix parmi les arbres de la forêt: il plante un pin, et la pluie le fait croître.
Yakan ka da itacen saifires, ko kuwa ya ɗauki saifires ko oak. Yă bar shi yă yi girma a cikin itatuwan kurmi, ko yă shuka itacen fir, ruwan sama kuma yă sa yă yi girma.
15 Et l'homme a de quoi brûler, et il en prend et se chauffe, et il en allume, et il cuit du pain. Il en fabrique aussi un Dieu, et il l'adore, et en taille une image, et il s'incline devant elle.
Abin hura wutar mutum ne; yakan ɗebi waɗansu yă hura wuta don yă ji ɗumi, ya hura wuta yă gasa burodi. Amma yakan ƙera zinariya yă kuma yi masa sujada; yakan yi gunki sa’an nan yă rusuna masa.
16 Il en brûle la moitié au feu, avec une moitié il apprête sa viande, rôtit son rôt, et se rassasie; il se chauffe aussi et dit: « Ah! ah! je me réchauffe! et je vois du feu! »
Rabin katakon yakan ƙone a wuta; a kansa yakan dafa abincinsa, yă gasa namansa yă kuma ci sai ya ƙoshi. Yakan ji ɗumi yă kuma ce, “Aha! Na ji ɗumi; na gan wutar.”
17 Et avec le reste il fait un dieu, son idole, et il s'incline devant elle, et il l'adore, et lui adresse sa prière, et dit: « Sauve-moi, car tu es mon Dieu! »
Da sauran itacen yakan yi allah, gunkinsa; yă rusuna masa yă kuma yi sujada. Yakan yi masa addu’a yă ce, “Ka cece ni; kai ne allahna.”
18 Ils n'ont ni connaissance, ni intelligence; car leurs yeux sont bouchés et ils ne voient pas, et leur cœur fermé et ils ne sentent pas.
Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba; an rufe idanunsu don kada su gani, tunaninsu kuma a rufe don kada su fahimta.
19 Il ne réfléchit pas, il n'a ni connaissance, ni intelligence pour dire: J'en ai brûlé la moitié au feu, et sur ses charbons j'ai aussi cuit mon pain, rôti ma viande, et l'ai mangée, et avec le reste ferais-je une abomination, devant une souche de bois me prosternerais-je?
Ba wanda yakan dakata ya yi tunani, ba wanda yake da sani ko fahimi ya ce, “Da rabinsa na yi amfani da shi don hura wuta; na ma gasa burodi a kan garwashinsa, na gasa nama na kuma ci. Ya kamata in yi abin ƙyama daga abin da ya rage? Ya kamata in rusuna wa guntun katako?”
20 Il se repaît de cendres, un cœur abusé le détourne de sauver son âme et de dire: N'est-ce pas un mensonge que je tiens dans ma main?
Yana cin toka, zuciyar da ta ruɗe tana ɓad da shi; ba zai iya cece kansa ba, ko ya ce, “Wannan abin da yake hannun dama na ba ƙarya ba ne?”
21 Souviens-t'en, Jacob, et Israël! car tu es mon serviteur, je t'ai formé; pour moi tu es un serviteur, Israël; tu ne seras pas oublié de moi!
“Tuna da waɗannan abubuwa, ya Yaƙub, gama kai bawana ne, ya Isra’ila. Na yi ka, kai bawana ne; Ya Isra’ila, ba zan manta da kai ba.
22 Je balaie comme un nuage tes crimes, et comme une nuée tes péchés: reviens à moi, car je te rachète!
Na shafe laifofinka kamar girgije, zunubanka kamar hazon safe. Ka komo wurina, gama na kuɓutar da kai.”
23 Cieux, retentissez de cantiques! car l'Éternel a agi; et vous, profondeurs de la terre, éclatez en acclamations! poussez des cris de joie, montagnes, avec les forêts et tous les arbres qui y sont! car l'Éternel rachète Jacob, et Il manifeste sa gloire sur Israël.
Ku rera don farin ciki, ya sammai, gama Ubangiji ya aikata wannan; ku yi sowa, ya duniya a ƙarƙashi. Ku ɓarke da waƙoƙi, ku duwatsu, ku jeji da dukan itatuwanku, gama Ubangiji ya kuɓutar da Yaƙub, ya nuna ɗaukakarsa a cikin Isra’ila.
24 Ainsi parle l'Éternel qui te rachète, et te forma dès l'origine de ta naissance: Je suis l'Éternel qui a tout créé, qui seul déploya les Cieux, et qui de moi-même étendis la terre,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarka, wanda ya yi ka a cikin mahaifa. “Ni ne Ubangiji, wanda ya yi dukan abubuwa, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya da kansa,
25 qui déjoue les présages des prophètes menteurs, et fais délirer les devins, qui fais reculer les sages, et change leur science en folie,
wanda ya sassāke alamun annabawan ƙarya ya masu duba suka zama wawaye, wanda ya tumɓuke koyon masu hikima ya mai da shi banza,
26 qui donne effet à la parole de mon serviteur, et accomplis les arrêts de mes envoyés, qui dis de Jérusalem: « Elle sera habitée, » et des villes de Juda: « Elles seront rebâties, et je relèverai leurs ruines! »
wanda ya tabbatar da maganganun bayinsa ya kuma cika annabce-annabcen’yan aikansa, “wanda ya ce game da Urushalima, ‘Za a zauna a cikinta,’ game da garuruwan Yahuda, ‘Za a gina su,’
27 qui dis à l'abîme: « Sèche, et je tarirai tes fleuves! »
wanda ya ce wa zurfin ruwaye, ‘Ku bushe, zan kuma busar da rafuffukanku,’
28 qui dis de Coresch: « Il est mon berger, et il exécutera toute ma volonté! » et qui dis de Jérusalem: « Qu'elle soit rebâtie! » et du Temple: « Qu'il soit fondé »
wanda ya yi zancen Sairus ya ce, ‘Shi ne makiyayina zan kuma cika dukan abin da na gan dama; zai yi zancen Urushalima cewa, “Bari a sāke gina ta,” game da haikali kuma cewa, “Bari a kafa harsashinsa.”’