< Aggée 1 >
1 La seconde année du roi Darius, le sixième mois, le premier jour du mois, la parole de l'Éternel fut adressée par Aggée, le prophète, à Zorobabel, fils de Salathiel, gouverneur de Juda, et à Josué, fils de Jéhotsadak, grand sacrificateur, en ces mots:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Ainsi parle l'Éternel des armées: Ce peuple dit: Le moment n'est pas encore venu, le moment où la maison de l'Éternel doit être rebâtie.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 C'est pourquoi la parole de l'Éternel fut adressée par Aggée, le prophète, en ces mots:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 Est-ce le moment pour vous-mêmes de vous loger dans vos maisons lambrissées, tandis que cette maison est en ruine?
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Or ainsi parle l'Éternel des armées: Soyez attentifs à la voie où vous êtes!
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Vous semez beaucoup et récoltez peu, vous mangez, mais non pas jusqu'à rassasiement, vous buvez, mais non pas votre soûl; vous avez des habits, mais non jusqu'à avoir chaud, et celui qui sert pour un gage, met ses gains dans une bourse trouée.
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Ainsi parle l'Éternel des armées: Soyez attentifs à la voie où vous êtes!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Montez à la montagne et en amenez du bois, et bâtissez la maison, afin que j'en aie du plaisir et que gloire me soit rendue, dit l'Éternel.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 Vous comptiez sur beaucoup, et voici, vous avez peu; et si vous l'amenez à la maison, je le dissipe. Pourquoi? dit l'Éternel des armées. A cause de ma maison qui est en ruine, tandis que vous êtes empressés chacun pour sa maison.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 C'est pourquoi au-dessus de vous les Cieux retiennent la rosée, et la terre retient son produit;
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 et j'ai appelé la sécheresse sur le pays et sur les montagnes, et sur le blé, et sur le moût, et sur l'huile, et sur tout ce que produit le sol, et sur l'homme, et sur le bétail, et sur tout le travail des mains.
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Et Zorobabel, fils de Salathiel, et Josué, fils de Jéhotsadak, grand sacrificateur, et tous les restes du peuple furent dociles à la voix de l'Éternel, leur Dieu, et aux paroles d'Aggée, le prophète, parce que l'Éternel, leur Dieu, l'avait envoyé, et le peuple eut crainte de l'Éternel.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Et Aggée, envoyé de l'Éternel, parla en vertu de la mission de l'Éternel au peuple en ces mots: Je suis avec vous, dit l'Éternel.
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 Et l'Éternel donna l'éveil à l'esprit de Zorobabel, fils de Salathiel, gouverneur de Juda, et à l'esprit de Josué, fils de Jéhotsadak, grand sacrificateur, et à l'esprit de tous les restes du peuple, et ils vinrent et se mirent à l'œuvre dans la maison de l'Éternel des armées, leur Dieu,
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 le vingt-quatrième jour du sixième mois, la seconde année du roi Darius.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,