< Genèse 9 >
1 Alors Dieu bénit Noé et ses fils, et leur dit: Soyez féconds et vous multipliez et remplissez la terre.
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 Et soyez craints et redoutés de tous les animaux de la terre et de tous les oiseaux des cieux, de tout ce qui rampe sur le sol et de tous les poissons de la mer: ils sont mis dans vos mains.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Tout ce qui se meut ayant vie, vous servira d'aliment; aussi bien que la verdure des plantes, je vous donne tout.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Ce n'est que la chair dans son âme, son sang, que vous ne mangerez point.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Et c'est votre sang seul qu'en faveur de votre vie je redemanderai; je le redemanderai à tous les animaux, et je redemanderai la vie de l'homme à l'homme, à son frère, quel qu'il soit.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Quiconque versera le sang de l'homme, par l'homme son sang sera versé, car Dieu a fait l'homme à son image.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Pour vous, soyez féconds et vous multipliez, et pullulez sur la terre et vous y multipliez.
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Et Dieu dit à Noé et à ses fils avec lui:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 Pour moi, voici, j'érige mon alliance avec vous et avec votre race après vous,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 et avec tous les êtres vivants qui sont à vos côtés, oiseaux, bétail et toute bête de la terre qui est à vos côtés, tous ceux qui sont sortis de l'arche avec vous, de tous les animaux de la terre.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 J'érige donc mon alliance avec vous à cet effet que dorénavant toute chair ne sera point exterminée par les eaux du déluge et que dorénavant il n'y aura plus de déluge pour détruire la terre.
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Et Dieu dit: Voici le signe de l'alliance que j'institue entre moi et vous et tous les êtres vivants qui sont à vos côtés, pour la suite des âges à jamais:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 je place mon arc dans la nuée pour qu'il devienne un signe d'alliance entre moi et la terre.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Et lorsque je ferai surgir les nuées sur la terre, et que mon arc apparaîtra dans la nuée,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 alors je me rappellerai l'alliance qui existe entre moi et vous et tous les êtres vivant en toute chair, et [qui stipule] que les eaux ne deviendront plus un déluge pour détruire toute chair.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 Et l'arc étant dans la nuée, je le regarderai pour me rappeler l'alliance éternelle qui existe entre Dieu et tout être vivant en toute chair qui se trouve sur la terre.
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Et Dieu dit à Noé: Tel est le signe de l'alliance que j'érige entre moi et toute chair qui se trouve sur la terre.
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Et les fils de Noé qui sortirent de l'arche étaient Sem, Cham et Japheth; or Cham était le père de Canaan.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Ce sont là les trois fils de Noé, et c'est d'eux qu'est issue la population répandue sur toute la terre.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Et Noé commença à être agriculteur et il planta de la vigne.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Et il but du vin, et il se trouva ivre et il se découvrit au milieu de sa tente.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Et Cham, père de Canaan, vit la nudité de son père, et le redit à ses deux frères dehors.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 Alors Sem et Japheth prirent le manteau et le mirent les deux sur leurs épaules, et marchèrent à reculons et couvrirent la nudité de leur père; mais leur visage était tourné, et ils ne virent point la nudité de leur père.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Et lorsque Noé se réveilla de son ivresse, il apprit ce que lui avait fait son fils cadet;
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 alors il dit: Maudit soit Canaan, Serviteur des serviteurs qu'il soit pour ses frères!
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Puis il dit: Béni soit l'Éternel, Dieu de Sem, et que Canaan soit son serviteur!
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Que Dieu donne de l'extension à Japheth, et qu'il habite dans les tentes de Sem, et que Canaan devienne leur serviteur!
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Et après le déluge Noé vécut trois cent cinquante ans;
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 et la totalité des jours de Noé fut neuf cent cinquante ans, puis il mourut.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.