< Esdras 4 >

1 Et lorsque les ennemis de Juda et de Benjamin apprirent que les enfants de la captivité bâtissaient un Temple à l'Éternel, Dieu d'Israël,
Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
2 ils se présentèrent à Zorobabel et aux chefs des maisons patriarcales et leur dirent: Nous voulons nous joindre à vous pour la bâtisse, car comme vous nous invoquons votre Dieu, et nous lui offrons des sacrifices depuis les jours d'Assarhaddon, roi d'Assyrie, qui nous a fait venir ici.
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
3 Mais Zorobabel et Jésuah et les autres chefs des maisons patriarcales d'Israël leur dirent: Ni vous ni nous n'avons le droit de bâtir [en commun] la Maison de notre Dieu; mais nous seuls nous élèverons l'édifice à l'Éternel, Dieu d'Israël, comme nous l'a recommandé le roi Cyrus, roi de Perse.
Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
4 Alors le peuple du pays ôta le courage au peuple de Juda en lui faisant peur de bâtir.
Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
5 Et ils soudoyèrent contre eux des Conseillers à l'effet de déjouer leur plan, et cela pendant tout [le reste de] la vie de Cyrus, roi de Perse, et jusqu'au règne de Darius, roi de Perse.
Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
6 Cependant sous le règne d'Assuérus, au début de son règne, ils écrivirent une accusation contre les habitants de Juda et de Jérusalem.
A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
7 Et au temps de Arthachsastha, Bislam, Mithredath, Tabeël et ses consorts écrivirent à Arthachsastha, roi de Perse. Or la lettre fut écrite en caractères araméens et traduite en araméen.
A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
8 Rehum, fondé de pouvoirs, et Simsaï, le Secrétaire, écrivirent contre Jérusalem au roi Arthachsastha une lettre ainsi conçue:
Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
9 « A cette date. — Rehum, fondé de pouvoirs, et Simsaï, le Secrétaire, et leurs autres collègues de Dina et Apharsatcha, Tarpela, Perse, Arach, Babel, Suse, Deha et Eilam,
Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
10 et les autres peuples qu'a déportés Osnappar, le grand et le puissant, et auxquels il a assigné un domicile dans la ville de Samarie, et les autres peuples en deçà du Fleuve et cætera. »
da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
11 C'est ici la copie de la lettre qu'ils lui envoyèrent à lui, au roi Arthachsastha: « Tes serviteurs, hommes d'au delà du Fleuve et caetera.
(Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
12 Notoire soit au Roi que les Juifs partis de chez toi sont venus vers nous à Jérusalem, qu'ils rebâtissent la ville séditieuse et méchante et en achèvent les murs et en restaurent les fondements.
Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
13 Or qu'il soit notoire au Roi que, si cette ville est relevée et les murs achevés, ils ne paieront pas le tribut, l'accise, ni les droits de route, et qu'ils frustreront d'autant le trésor royal.
Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
14 Puis donc que nous mangeons le sel du palais, et que nous ne pouvons être plus longtemps témoins du dommage du Roi, en conséquence nous t'adressons ce message et faisons savoir au Roi,
Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
15 que l'on recherche dans le livre des Annales de tes pères, et dans le livre des Annales tu trouveras et apprendras que cette ville a été une ville séditieuse et funeste aux rois et aux provinces et qu'on y a comploté la révolte dès les jours d'autrefois: ensuite de quoi cette ville a été détruite.
domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
16 Nous faisons savoir au Roi que, si cette ville est relevée et ses murs achevés, il résultera que de ce côté du Fleuve tu n'auras plus de possessions. »
Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
17 Alors le roi expédia un rescrit à Rehum, le fondé de pouvoirs, et à Simsaï, le Secrétaire, et à leurs autres collègues habitant Samarie, et aux autres en deçà du Fleuve: « Salut et cætera.
Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
18 La lettre que vous nous avez envoyée a été lue exactement devant moi.
An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
19 Et de ma part ordre a été donné de faire des recherches, et l'on a trouvé que cette ville dès les jours d'autrefois s'est soulevée contre les Rois et que la révolte et la sédition y ont été pratiquées.
Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
20 Et des Rois puissants ont été à Jérusalem et ont régné sur tout ce qui est au delà du Fleuve, et tribut, accise et droits de route leur ont été payés.
Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
21 En conséquence, donnez l'ordre d'empêcher ces gens de rebâtir cette ville jusqu'à ce que de moi un ordre en émane.
Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
22 Et prenez garde de manquer d'agir en conséquence. Et pourquoi le dommage s'accroîtrait-il au détriment du roi? »
Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
23 Là-dessus, dès que la copie de la lettre du roi Arthachsastha eut été lue devant Rehum et Simsaï, le Secrétaire, et leurs collègues, ils se rendirent en hâte à Jérusalem auprès des Juifs et ils les arrêtèrent de main forte.
Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
24 Dès lors cessèrent les travaux à la Maison de Dieu à Jérusalem, et ils furent entravés jusqu'à la seconde année du règne de Darius, roi de Perse.
Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.

< Esdras 4 >