< Ézéchiel 25 >
1 Et la parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, tourne ton visage contre les enfants d'Ammon et prophétise contre eux,
“Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
3 et dis aux enfants d'Ammon: Écoutez la parole du Seigneur, l'Éternel! Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que tu as dit: « Ah! ah! » à la vue de mon sanctuaire profané et du pays d'Israël désolé, et de la maison de Juda menée en captivité;
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
4 pour cela, voici, je te donne aux enfants de l'Orient en propriété, pour qu'ils établissent leurs parcs au milieu de toi, et y fixent leurs demeures; ils mangeront tes fruits et boiront ton lait:
saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
5 et je ferai de Rabbah un pâturage pour les chameaux, et [du pays] des enfants d'Ammon une bergerie pour les brebis, et vous saurez que je suis l'Éternel.
Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
6 Car ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que tu as battu des mains et frappé du pied, et qu'avec tout ton orgueil tu t'es réjouie de cœur à la vue du pays d'Israël;
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
7 pour cela, voici, j'étends ma main contre toi, et te livre en proie aux nations, et te retranche du nombre des peuples, et t'extermine du milieu des pays; je t'anéantis, afin que tu saches que je suis l'Éternel.
saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
8 Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que Moab et Séir disent: Voici, la maison de Juda est comme tous les autres peuples!
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
9 pour cela, voici j'ouvre le flanc de Moab, depuis les villes, depuis toutes ses villes, ornement du pays, Beth-Jésimoth, Baal-Meon et jusqu'à Kiriathaïm,
saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
10 aux enfants de l'Orient, en même temps que le pays des enfants d'Ammon, et je le leur donnerai en propriété, afin qu'il ne soit plus fait mention des enfants d'Ammon parmi les peuples;
Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
11 et sur Moab j'exécuterai mes jugements, afin qu'ils sachent que je suis l'Éternel.
zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
12 Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que Édom s'est conduit envers la maison de Juda par un esprit de vengeance, et s'est rendu coupable, et a tiré vengeance d'elle;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
13 pour cela, ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: J'étendrai ma main contre Édom, et en exterminerai les hommes et les bêtes, et j'en ferai un désert de Théman à Dedan; ils périront par l'épée.
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
14 Et j'exécuterai mes vengeances sur Édom par le bras de mon peuple d'Israël, et il traitera Édom selon ma colère et mon courroux, et ils ressentiront mes vengeances, dit le Seigneur, l'Éternel.
Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 Ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Parce que les Philistins ont agi par vengeance et qu'ils se sont vengés orgueilleusement et de cœur, avec la volonté de détruire, par suite d'une haine éternelle;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
16 pour cela, ainsi parle le Seigneur, l'Éternel: Voici, j'étends ma main contre les Philistins, et j'extirperai les Crétites, et détruirai ce qui reste sur la côte de la mer,
saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
17 et j'exercerai sur eux de grandes vengeances en châtiant avec fureur, afin qu'ils sachent que je suis l'Éternel, quand j'exercerai mes vengeances sur eux.
Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”