< 2 Samuel 5 >
1 Et toutes les Tribus d'Israël firent une démarche auprès de David à Hébron et parlèrent en ces termes: Voici, nous sommes tes os et ta chair.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 Ci-devant déjà, quand Saül régnait sur nous, c'est toi qui menais et ramenais Israël, et l'Éternel t'a dit: Tu seras le pasteur de mon peuple d'Israël et tu deviendras prince d'Israël.
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 Tous les Anciens d'Israël se présentèrent donc chez le Roi à Hébron, et le Roi David conclut avec eux un pacte à Hébron devant l'Éternel, et ils oignirent David comme Roi d'Israël.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 David avait trente ans à son avènement, et il régna quarante ans.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 A Hébron il régna sur Juda sept ans et six mois, et à Jérusalem il régna trente-trois ans sur la totalité d'Israël et de Juda.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 Et le Roi avec ses hommes marcha sur Jérusalem contre les Jébusites habitants du pays. Et ils tinrent à David ce langage: Tu ne saurais pénétrer ici, mais les aveugles et les perclus te tiendraient à distance! pour dire: David ne pénétrera pas ici.
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 Cependant David s'empara de la citadelle de Sion, c'est la Cité de David.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 Et David avait dit en ce jour-là: Quiconque battra les Jébusites et s'avancera jusqu'à l'aqueduc et aux perclus et aux aveugles hostiles à la personne de David… (De là le dicton: Ni aveugle ni perclus n'entrera au logis.)
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 Et David prit sa résidence dans la citadelle qu'il appela Cité de David; et David fit des constructions tout autour à partir de Millo jusque dans l'intérieur.
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 Et David allait grandissant pas à pas, et l'Éternel, Dieu des armées, l'assistait.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 Et Hiram, roi de Tyr, envoya une députation à David, et du bois de cèdre et des charpentiers et des maçons, qui bâtirent une maison à David.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 Et David sentit que l'Éternel le confirmait comme roi d'Israël, et qu'il élevait son royaume en vue de son peuple d'Israël.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 Et David prit encore des concubines et des femmes de Jérusalem après être venu d'Hébron; et il naquit encore à David des fils et des filles.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 Or voici les noms de ses enfants nés à Jérusalem: Sammuah et Sobab et Nathan et Salomon,
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 et Jibehar, et Elisuah et Népheg et Japhiah
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 et Elisamah et Eliada et Eliphélet.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 Et à la nouvelle de l'onction de David en qualité de roi d'Israël les Philistins en totalité se mirent en campagne à la recherche de David.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 Et David en ayant eu avis descendit au fort. Et les Philistins parurent et occupèrent la vallée de Rephaïm.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 Alors David interrogea l'Éternel en ces termes: Irai-je attaquer les Philistins? les feras-tu tomber dans mes mains? Et l'Éternel dit à David: Va, car je ferai tomber les Philistins dans tes mains.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 Et David s'avança sur Bahal-Peratsim où il les défit; et il dit: L'Éternel a rompu mes ennemis devant moi comme des eaux dont on rompt le fil. C'est pourquoi il donna à ce lieu le nom de Bahal-Peratsim (lieu des ruptures).
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 Et ils abandonnèrent leurs idoles, et David et ses hommes les emportèrent.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 Et les Philistins renouvelèrent l'attaque et occupèrent la vallée de Rephaïm.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 Et David interrogea l'Éternel qui répondit: N'attaque pas! tourne-les et les prends à dos et joins-les vis-à-vis des baumiers-pleureurs.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 Et lorsque tu ouïras un bruit de pas dans les cimes des baumiers-pleureurs, alors dépêche-toi! car c'est le moment où l'Éternel marchera devant toi à la défaite de l'armée des Philistins.
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 Et David se conforma à l'ordre de l'Éternel et il battit les Philistins, de Geba aux abords de Gézer.
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.