< 2 Samuel 11 >

1 Et au retour de l'année, à l'époque où les Rois ouvraient la campagne, David envoya Joab et avec lui ses serviteurs et tout Israël; et ils ravagèrent le pays des Ammonites et mirent le siège devant Rabba.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Mais David resta à Jérusalem. Et il advint que dans la soirée David s'étant levé de son lit de repos, se promenait sur le toit de la demeure royale; et de cette terrasse il aperçut une femme au bain; et cette femme, de figure, était belle au plus haut point.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 Et David envoya demander qui était cette femme, et on dit: Mais, c'est Bathséba, fille d'Eliam, femme d'Urie, le Héthien.
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 Et David dépêcha des émissaires chargés de l'emmener; et elle entra chez lui, et il habita avec elle; puis, elle accomplit la pratique sainte pour secouer sa souillure, et elle s'en retourna dans sa maison.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 Et elle se trouva enceinte, et elle en fit informer David en ces termes: Je suis enceinte.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Alors David fit dire à Joab: Envoie-moi Urie, le Héthien. Et Joab envoya Urie à David.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Et Urie étant arrivé chez lui, David le questionna sur l'état de Joab, et sur l'état de l'armée, et sur l'état des opérations.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Et David dit à Urie: Descends chez toi et te baigne les pieds. Et Urie sortit du palais du Roi, et il fut suivi d'un don du Roi.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Mais Urie se coucha à la porte du palais du Roi avec tous les serviteurs de son maître, et ne descendit point à son logis.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Et l'on informa David en ces termes: Urie n'est point descendu chez lui. Et David dit à Urie: N'arrives-tu pas de voyage? Pourquoi n'es-tu pas descendu chez toi?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Et Urie dit à David: L'Arche et Israël et Juda logent dans des huttes, et mon seigneur Joab et les serviteurs de mon seigneur campent sur le sol; et moi, j'entrerais dans ma maison pour manger et boire et coucher aux côtés de ma femme! Par ta vie et la vie de ton âme! non, je n'en ferai rien.
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Et David dit à Urie: Reste ici encore aujourd'hui, et demain je te congédierai. Urie resta donc à Jérusalem ce jour-là et le suivant.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Et David le convia; et il mangea devant lui et but; et David l'enivra. Mais le soir il sortit pour se coucher sur son lit à côté des serviteurs de son maître, et il ne descendit point dans sa maison.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Et le lendemain, David écrivit à Joab une lettre qu'il lui expédia par Urie.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Et dans cette lettre il marquait: Exposez Urie au plus fort de la mêlée, puis retirez-vous de ses côtés, pour qu'il soit atteint et meure.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Et comme Joab faisait le siège de la ville, il plaça Urie à l'endroit où il savait qu'il y avait des braves.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Et les hommes de la ville firent une sortie et en vinrent aux prises avec Joab, et la troupe, les serviteurs de David, eurent des hommes tués, et Urie, le Héthien, fut aussi du nombre des morts.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Là-dessus Joab envoya à David un rapport de toutes les circonstances de l'affaire.
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 Et il donna au messager cette instruction: Quand tu auras fini de raconter au Roi tous les détails de l'engagement,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 si la colère monte au Roi et qu'il te dise: Pourquoi vous approcher de la ville pour une attaque? ne saviez-vous pas qu'ils tireraient du haut de la muraille?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Qui a abattu Abimélech, fils de Jérubbéseth? n'est-ce pas une femme qui du haut du mur lui a lancé un fragment de meule, et il en est mort à Thébets? pourquoi vous approcher de la muraille? — alors dis-lui: Ton serviteur Urie, le Héthien, est mort aussi.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Le courrier partit, et arrivé il redit à David tout ce dont Joab l'avait chargé.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Et le messager dit à David: Comme les gens de la ville nous avaient fortement attaqués et avaient dirigé contre nous une sortie dans les champs, nous les avons refoulés jusqu'à l'abord de la porte,
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 c'est alors que du haut du mur les archers ont tiré sur tes serviteurs et que plusieurs des serviteurs du Roi ont péri, et ton serviteur Urie, le Héthien, a aussi succombé.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Alors David dit au messager: Voici ce que tu as à dire à Joab: Ne sois point peiné de cette affaire! car par-ci, par-là l'épée tranche: pousse avec vigueur l'assaut de la place et la rase! — Et encourage-le!
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Et la femme d'Urie apprenant la mort d'Urie, son mari, prit le deuil pour son seigneur.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Et à l'expiration du deuil, David la fit chercher et l'introduisit dans sa maison, et elle devint sa femme et lui enfanta un fils. Mais l'action que David avait faite, déplut à l'Éternel.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >