< 2 Rois 3 >
1 Cependant Joram, fils d'Achab, devint roi d'Israël à Samarie la dix-huitième année de Josaphat, roi de Juda, et régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Et il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, seulement pas au même degré que son père et que sa mère, et il fit disparaître les statues de Baal qu'avait faites son père.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Il s'adonna seulement aux péchés de Jéroboam, fils de Nebat, qui avait entraîné Israël au péché; il ne s'en départit pas.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Or Mésa, roi de Moab, était propriétaire de troupeaux et payait au roi d'Israël un tribut de cent mille agneaux et cent mille béliers avec la toison.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Mais à la mort d'Achab le roi de Moab se rebella contre le roi d'Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Et à cette occasion le roi Joram sortit de Samarie et passa en revue tous les Israélites;
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 puis il se mit en mouvement et députa vers Josaphat, roi de Juda, pour lui dire: Le roi de Moab s'est rebellé contre moi; veux-tu marcher avec moi contre Moab pour l'attaquer? Et il répondit: Je marcherai, moi comme toi, mon monde comme ton monde, mes chevaux comme tes chevaux.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Et il dit: Quel chemin prendrons-nous? Et il répliqua: Le chemin du désert d'Edom.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Ainsi, se mirent en marche le roi d'Israël et le roi de Juda et le roi d'Edom, et après une traite de sept jours, l'eau manqua pour l'armée et le bétail qui les suivait.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Alors le roi d'Israël dit: Hélas! l'Éternel a fait appel à ces trois rois pour les mettre dans la main de Moab.
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Et Josaphat dit: N'y a-t-il ici aucun prophète de l'Éternel pour consulter l'Éternel par son moyen? Et l'un des serviteurs du roi d'Israël répondit et dit: Il y a ici Elisée, fils de Schaphat, qui versait l'eau sur les mains d'Elie.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Et Josaphat dit: La parole de l'Éternel est chez lui! Là-dessus le roi d'Israël et Josaphat et le roi d'Edom descendirent auprès de lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Mais Elisée dit au roi d'Israël: Qu'ai-je à faire avec toi? Va aux prophètes de ton père et aux prophètes de ta mère! Et le roi d'Israël lui dit: Non! car c'est l'Éternel qui a fait appel à ces trois rois pour les mettre dans la main de Moab.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Et Elisée dit: Par la vie de l'Éternel des armées, aux ordres de qui je suis, si je n'avais égard à Josaphat, roi de Juda, je ne te regarderais pas, je ne te verrais pas!
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Eh bien! amenez-moi un joueur de luth. Et comme le joueur de luth touchait les cordes, la main de l'Éternel s'étendit sur lui
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 et il dit: Ainsi parle l'Éternel: Pratiquez dans ce ravin fossés et fossés.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car ainsi parle l'Éternel: Vous ne verrez ni vent ni pluie, et ce ravin s'emplira d'eau, et vous vous désaltérerez, vous et vos troupeaux et votre bétail.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Mais c'est trop peu aux yeux de l'Éternel: Il mettra Moab dans votre main.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Et vous forcerez toutes les villes fortes et toutes les villes d'élite, et vous abattrez tous les meilleurs arbres, et comblerez toutes les sources, et vous affligerez de pierres tous les champs fertiles.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Et le matin au moment de l'oblation de l'offrande, voilà que l'eau arriva du chemin d'Edom, et toute la contrée fut pleine d'eau.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Cependant lorsque tous les Moabites apprirent que les rois s'avançaient pour les attaquer, ils furent tous convoqués depuis les hommes à même de porter les armes et au-dessus, et ils se portèrent à la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Et à leur lever le matin, quand le soleil parut sur les eaux, les Moabites virent devant eux l'eau rouge comme le sang,
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 et ils dirent: C'est du sang! les rois se sont détruits l'un l'autre et se sont massacrés entre eux; au pillage donc, Moabites!
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Mais lorsqu'ils arrivèrent au camp d'Israël, les Israélites se levèrent et défirent les Moabites qui s'enfuirent devant eux, et [les Israélites] pénétrèrent dans le pays et mirent Moab en déroute.
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 Et ils démolirent les villes, et ils jetèrent chacun sa pierre sur tous les champs fertiles qu'ils en remplirent, et comblèrent toutes les sources et abattirent tous les meilleurs arbres, jusqu'à ne laisser que les pierres de la ville à Kir-Haréseth. Et les frondeurs l'enveloppèrent et la battirent.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Et lorsque le roi de Moab vit que la bataille était plus forte que lui, il prit avec lui sept cents hommes tirant l'épée pour percer jusqu'au roi d'Edom; mais ils ne purent.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Alors il prit son fils premier-né, qui devait régner en sa place, et l'immola en holocauste sur le rempart. Et il y eut une grande indignation contre les Israélites, qui partirent et regagnèrent le pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.