< 2 Rois 17 >
1 La douzième année d'Achaz, roi de Juda, Hosée, fils d'Éla, devint roi d'Israël à Samarie, pour neuf ans.
A shekara ta goma sha biyu ta mulkin Ahaz sarkin Yahuda, Hosheya ɗan Ela ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki na shekara tara.
2 Et il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, seulement pas à l'égal des rois d'Israël, ses prédécesseurs.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar na sarakunan Isra’ilan da suka riga shi ba.
3 Contre lui s'avança Salmanassar, roi d'Assyrie, et Hosée lui fut assujetti, et lui paya un tribut.
Shalmaneser sarkin Assuriya ya kawo wa Hosheya wanda dā abokin tarayyarsa ne, hari har Hosheya ya biya shi haraji.
4 Mais le roi d'Assyrie découvrit une menée chez Hosée, lequel envoyait des messagers à So, roi d'Egypte, et ne payait point le tribut au roi d'Assyrie année par année; c'est pourquoi le roi d'Assyrie le fit prisonnier et le mit aux fers dans un cachot.
Amma sarkin Assuriya ya gane cewa Hosheya mai cin amana ne, gama ya aika da wakilai wurin So sarkin Masar, ya kuma daina aika wa sarkin Assuriya haraji yadda ya saba yi kowace shekara. Saboda haka Shalmaneser ya kama shi ya sa a kurkuku.
5 Et le roi d'Assyrie s'avança sur tout le pays, et marcha contre Samarie qu'il assiégea trois ans.
Sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar Hosheya gaba ɗaya farmaki, ya kewaye Samariya na tsawon shekara uku.
6 La neuvième année d'Hosée le roi d'Assyrie prit Samarie et déporta les Israélites en Assyrie, et les établit à Chala et au Chabor, fleuve de Gozan, et dans les villes des Mèdes.
A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, sarkin Assuriya ya ci Samariya da yaƙi ya kuma kwashe Isra’ilawa zuwa Assuriya. Ya tsugunar da su a Hala, da a Gozan a bakin Kogin Habor da kuma a garuruwan Medes.
7 C'est que les enfants d'Israël s'étaient rendus coupables envers l'Éternel, leur Dieu, qui les avait retirés du pays d'Egypte, de dessous la main de Pharaon, roi d'Egypte, et qu'ils révérèrent des dieux différents.
Duk wannan ya faru ne saboda Isra’ilawa sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fitar da su daga Masar daga ƙarƙashin ikon Fir’auna sarkin Masar. Sun yi wa waɗansu alloli sujada
8 Et ils suivirent les us des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël, et des rois d'Israël qui les avaient institués.
suka kuma bi gurbin al’umman da Ubangiji ya kora a gabansu, da kuma ayyukan da sarakuna Isra’ila suka gabatar.
9 Et les enfants d'Israël firent parade de choses qui ne sont pas bien, en opposition à l'Éternel, leur Dieu, et s'élevèrent des tertres dans toutes leurs villes, depuis les tours d'observation aux places fortes.
Isra’ilawa a ɓoye sun aikata abubuwan da ba daidai ba ga Ubangiji Allahnsu. Tun daga hasumiyoyi har zuwa birane masu katanga, sun gina wa kansu wuraren sujada na tudu a dukan garuruwansu.
10 Et ils se dressèrent des colonnes et des Astartés sur toute colline éminente, et sous tout arbre vert.
Suka kafa keɓaɓɓun duwatsu da kuma ginshiƙan Ashera a kowane tudu mai tsayi da kuma a ƙarƙashin kowane babban itace.
11 Et là ils offrirent l'encens sur tous les tertres comme les nations que l'Éternel avait exilées devant eux, et pratiquèrent des choses mauvaises pour provoquer l'Éternel.
Suka ƙona turare a kan kowane tudu, kamar dai yadda al’umman da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka yi muguntan da ya sa Ubangiji ya yi fushi.
12 Et ils servirent les idoles dont l'Éternel leur avait dit: Vous n'en ferez rien.
Suka bauta wa gumaka, ko da yake Ubangiji ya ce, “Ba za ku yi wannan ba.”
13 Et l'Éternel somma Israël et Juda par l'organe de tous ses prophètes, de tout Voyant, en ces termes: Quittez vos voies mauvaises et gardez mes commandements, mes statuts, d'après toute la Loi que j'ai prescrite à vos pères, et tous les messages que je vous ai envoyés par l'organe de mes serviteurs les prophètes!
Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
14 Mais ils n'écoutèrent point, ils roidirent leur col comme le col de leurs pères, qui n'avaient pas cru en l'Éternel, leur Dieu.
Amma ba su saurare ni ba don sun kangare kamar kakanninsu, waɗanda ba su amince da Ubangiji Allahnsu ba.
15 Et ils méprisèrent ses statuts et son alliance qu'il avait conclue avec leurs pères, et ses sommations qu'il leur adressait, et ils suivirent les vaines idoles et s'adonnèrent à la vanité, et imitèrent les nations de leurs alentours que l'Éternel leur avait commandé de ne point imiter.
Suka yi watsi da farillansa da yarjejjeniyar da ya ƙulla da kakanninsu, da kuma kashedin da ya yi musu. Suka bi gumaka marasa amfani, wannan ya sa su ma kansu suka zama marasa amfani. Suka kwaikwayi sauran ƙasashen da suke kewaye da su, ko da yake Ubangiji ya umarce su cewa, “Kada ku yi rayuwa irin tasu,” suka kuwa yi abin da Ubangiji ya hana su.
16 Et ils négligèrent tous les commandements de l'Éternel, leur Dieu, et se fabriquèrent des images de fonte, deux veaux, et ils se firent des Astartés, et adorèrent toute l'armée des cieux, et rendirent un culte à Baal.
Suka wofinta dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu gumakan zubi na siffar’yan maruƙa biyu, da kuma ginshiƙin Ashera. Suka rusuna wa rundunan taurari, suka kuma yi wa Ba’al sujada.
17 Et ils firent passer par le feu leurs fils et leurs filles et pratiquèrent la divination et les augures et se vendirent pour faire ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, afin de le provoquer.
Suka miƙa’ya’yansu maza da mata hadaya ta wuta. Suka yi duba, suka yi sihiri suka kuma ba da kansu ga mugunta a gaban Ubangiji; suka sa ya yi fushi.
18 Alors l'Éternel se courrouça fort contre Israël et Il les exclut de sa présence: il ne resta que la tribu de Juda seule.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi ƙwarai da Isra’ila, ya kuma kawar da su daga gabansa. Kabilar Yahuda kaɗai aka bari,
19 Même Juda ne garda pas les commandements de l'Éternel, leur Dieu; ils marchèrent d'après les statuts dressés par les Israélites.
ko Yahuda ma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba. Sun bi gurbin da Isra’ila ta kawo.
20 Ce qui fit que l'Éternel répudia la totalité de la race d'Israël qu'il humilia et livra à la merci des spoliateurs jusque-là qu'il les bannit de sa présence.
Saboda haka Ubangiji ya wofinta mutanen Isra’ila; ya azabtar da su, ya kuma ba da su a hannun masu kwasar ganima, sai da ya shafe su ƙaƙaf daga gabansa.
21 C'est pourquoi Israël avait fait scission avec la maison de David, et s'était donné pour roi Jéroboam, fils de Nebat, et Jéroboam avait débauché Israël du service de l'Éternel et l'avait entraîné à un péché grand.
Sa’ad da ya ware Isra’ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat sarki a kansu. Yerobowam ya rinjayi Isra’ila daga ƙin Ubangiji, ya sa suka aikata babban zunubi.
22 Et les enfants d'Israël persistèrent dans tous les péchés de Jéroboam, que celui-ci avait commis, et ne s'en départirent pas,
Isra’ila suka nace cikin dukan zunuban Yerobowam, ba su kuwa rabu da su ba
23 jusque là que l'Éternel exclut Israël de sa présence, comme Il avait dit par l'organe de tous ses serviteurs les prophètes, et Israël fut déporté de son pays en Assyrie; ce qu'il est encore aujourd'hui.
har Ubangiji ya kawar da su daga gabansa, kamar yadda ya gargaɗe su ta bakin bayinsa annabawa. Saboda haka aka kwashi mutanen Isra’ila daga ƙasarsu zuwa bauta a Assuriya, har wa yau kuwa suna can.
24 Et le roi d'Assyrie fit venir [du monde] de Babel et de Cutha et de Arva et de Hamath et de Sepharvaïm, et il l'établit dans les villes de la Samarie en place des enfants d'Israël; et ils prirent possession de la Samarie et se domicilièrent dans les villes.
Sarkin Assuriya ya kawo mutane daga Babilon, Kuta, Afa, Hamat da Sefarfayim ya zaunar da su a garuruwan Samariya don su maya gurbin Isra’ilawa. Suka mallaki Samariya suka kuma zauna a garuruwansu.
25 Et il arriva au début de l'établissement de ces gens qui ne craignaient pas l'Éternel, que l'Éternel envoya contre eux les lions, qui firent du carnage parmi eux.
Sa’ad da suka fara zama a can, ba su bauta wa Ubangiji ba; saboda haka ya aika da zakoki a tsakaninsu suka karkashe waɗansu mutane.
26 Alors ils s'adressèrent au roi d'Assyrie en ces termes: Les nations que tu as transportées et établies dans les villes de la Samarie, ne connaissent pas le rite du dieu du pays: aussi a-t-il envoyé contre eux les lions qui, voici, les tuent, parce qu'ils ignorent, le rite du dieu du pays.
Sai aka faɗa wa sarkin Assuriya cewa, “Mutanen da ka kwashe ka zaunar a garuruwan Samariya fa ba su san abin da allahn ƙasar yake bukata ba. Saboda haka allahn ƙasar ya tura zakoki a cikinsu, waɗanda suke karkashe su, domin mutanen ba su san abin da yake bukata ba.”
27 Et le roi d'Assyrie donna cet ordre: Ramenez-y l'un des prêtres que vous avez emmenés de là en captivité; afin qu'ils puissent aller y habiter étant initiés [par le prêtre] au rite du dieu du pays.
Sai sarkin Assuriya ya ba da umarni cewa, “A sami wani daga cikin firistocin da aka kwaso zuwa bauta daga Samariya, yă koma yă zauna a can, yă koya wa mutanen abin da allahn ƙasar yake bukata.”
28 Il vint donc un des prêtres qu'ils avaient emmenés de Samarie, et il se fixa à Béthel, et il leur enseigna comment ils devaient célébrer le culte de l'Éternel.
Saboda haka ɗaya daga cikin firistocin da aka kawo bauta daga Samariya ya dawo ya zauna a Betel, ya koya musu yadda za su yi sujada ga Ubangiji.
29 Cependant chaque peuplade se faisait d'ailleurs son dieu, et elles les placèrent dans les temples des tertres élevés par les Samaritains, chacune dans les villes où elle était établie.
Duk da haka, jama’ar kowace ƙasa, suka ƙera tasu alloli a garuruwa masu yawa inda suke zaune, suka sa su a masujadan da mutanen Samariya suka gina a kan tuddai.
30 Et les gens de Babel firent des loges de filles, et les gens de Cuth [l'idole] Nergal, et les gens de Hamath, Asima,
Mutane daga Babilon suka ƙera Sukkot Benot, mutane daga Kut suka ƙera Nergal, mutane daga Hamat suka ƙera Ashima;
31 et les Avites, Nibchaz et Thirthak, et les Sepharvites brûlaient leurs fils dans le feu à Adrammelech et Anammelech, divinités de Sepharvaïm.
Awwiyawa suka ƙera Nibhaz da Tartak, Sefarfayawa kuwa suka ƙone’ya’yansu a wuta a matsayi hadayu ga Adrammelek da Anammelek allolin Sefarfayim.
32 Et ils rendaient aussi un culte à l'Éternel, et se créèrent de leur sein des prêtres pour les tertres, qui sacrifiaient pour eux dans les temples des tertres.
Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka zaɓi mutanensu su yi musu hidima a matsayin firistoci a masujadan da suke kan tuddai.
33 Ils rendaient un culte à l'Éternel et servaient leurs dieux selon le rite des nations d'où on les avait transportés.
Sun yi wa Ubangiji sujada, amma kuma sun bauta wa allolinsu bisa ga al’adun ƙasashen da suka fito.
34 Jusqu'aujourd'hui leur pratique est conforme à leurs premiers usages; ils ne rendent point un culte à l'Éternel [seul]; et n'agissent point [uniquement] d'après leurs us, et coutumes, nom plus que d'après la Loi et le Commandement prescrit par l'Éternel aux fils de Jacob à qui Il avait donné le nom d'Israël.
Har yă zuwa yau, sun nace da ayyukansu na dā. Ba sa yin wa Ubangiji sujada, ba sa kuma bin dokoki da farillansa, dokoki da umarnan da Ubangiji ya ba wa zuriyar Yaƙub, wadda ya ba wa suna Isra’ila.
35 Car l'Éternel avait conclu une alliance avec eux, et leur avait donné cet ordre: Vous ne craindrez pas d'autres dieux et vous ne les adorerez pas et ne les servirez pas et ne leur ferez pas de sacrifices;
Da Ubangiji ya ƙulla alkawari da Isra’ilawa, ya dokace su cewa, “Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada ko ku durƙusa a gabansu ku bauta musu, ko ku miƙa musu hadaya.
36 mais l'Éternel, qui vous a retirés du pays d'Egypte avec une grande puissance et le bras étendu, c'est Lui que vous craindrez, adorerez, Lui à qui vous offrirez des sacrifices;
Amma Ubangiji wanda ya fito da ku daga Masar da iko mai girma da hannu mai ƙarfi, shi ne za ku yi masa sujada. Gare shi za ku durƙusa ku kuma miƙa masa hadayu.
37 et les statuts et les rites et la Loi et le Commandement qu'il vous a donnés par écrit, c'est ce que vous observerez pour le pratiquer en tout temps, sans craindre d'autres dieux;
Dole kullum ku mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da farillan, dokoki da umarnan da ya rubuta muku. Kada ku yi wa waɗansu alloli sujada.
38 et l'alliance que J'ai conclue avec vous, vous ne l'oublierez pas, et vous ne craindrez pas d'autres dieux;
Kada ku manta da alkawarin da na ƙulla da ku, kada ku yi sujada ga waɗansu alloli.
39 mais l'Éternel, votre Dieu, vous le craindrez, et Il vous sauvera de la main de tous vos ennemis.
Maimakon haka, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada; shi ne zai cece ku daga hannun abokan gābanku.”
40 Mais ils n'obéirent pas; au contraire, ils se réglèrent d'après leurs premiers usages.
Amma ba su saurara ba, suka nace da ayyukansu na dā.
41 C'est ainsi que ces nations, tout en rendant un culte à l'Éternel, servaient leurs idoles, et leurs enfants et petits-enfants agissent aujourd'hui encore, comme ont agi leurs pères.
Ko ma yayinda mutanen nan suke yi wa Ubangiji sujada, ba su daina bauta wa gumakansu ba. Har yă zuwa yau,’ya’yansu da jikokinsu sun ci gaba da bin gurbin kakanninsu.