< 1 Samuel 21 >
1 Et David vint à Nob, chez Ahimélech, le Prêtre; et Ahimélech accourut au devant de David et lui dit: Pourquoi es-tu seul, sans personne avec toi?
Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
2 Et David répondit au Prêtre Ahimélech: Le Roi m'a chargé d'une affaire et m'a dit: Personne ne doit rien savoir de l'affaire pour laquelle je te dépêche, non plus que des instructions que je t'ai données. Et j'ai marqué aux gens de ma suite un certain lieu pour rendez-vous.
Dawuda ya ce wa Ahimelek firist, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya sa in yi. Na faɗa wa mutanena inda za su same ni.
3 Et maintenant ce que tu as sous la main, donne-le moi, cinq pains ou ce qui se trouvera.
Yanzu, me kake da shi a hannu? Ka ba ni burodi guda biyar, ko wani abu da kake da shi a nan.”
4 Et le Prêtre répondit à David et lui dit: Je n'ai pas sous la main de pain ordinaire; il n'y a que du pain sacré; si tes gens s'étaient seulement abstenus de femmes!
Amma firist ya ce wa Dawuda, “Ba ni da burodi iri na kowa da kowa, sai dai akwai burodin da aka tsarkake. Za ka iya ɗauka ku ci idan mutanenka ba su kwana da mata ba.”
5 Et David répondit au Prêtre et lui dit: Ce qui est certain, c'est que depuis nombre de jours tout accès auprès des femmes nous est fermé, et à mon départ mes gens avaient leurs personnes en état de sainteté, et l'usage profane que nous voulons faire d'une chose sacrée, sera aujourd'hui sanctifié par l'état de nos personnes.
Dawuda ya ce, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena sukan keɓe kansu a koyaushe suka tashi’yar tafiya, balle fa a yau!”
6 Alors le Prêtre lui remit le pain sacré, car il n'y avait là pas d'autre pain que le pain de présentation, qu'on avait enlevé de devant l'Éternel pour substituer au moment même du pain chaud à celui qu'on ôtait.
Don haka firist ya ba shi keɓaɓɓen burodi, tun da yake babu wani burodi a can sai dai burodin Kasancewa da aka cire daga gaban Ubangiji, aka sa burodi mai zafi a maimakon wanda aka cire a ranar.
7 [Or là se trouvait en ce jour un homme d'entre les serviteurs de Saül, séquestré devant l'Éternel; il se nommait Doëg, était Iduméen et grand-maître des bergers de Saül].
A ranar kuwa, ɗaya daga cikin bayin Shawulu yana can, a tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom, shugaban makiyayan Shawulu.
8 Et David dit à Ahimélech: N'as-tu pas à ta portée une pique ou une épée? Car je n'ai pris avec moi ni mon épée ni mon équipement, car la commission du Roi était pressante.
Dawuda ya ce wa Ahimelek, “Ba ka da māshi ko takobi a nan? Ban kawo māshina ko wani makami ba gama saƙon sarki ya zo mini da gaggawa.”
9 Et le Prêtre dit: L'épée de Goliath, le Philistin, que tu as fait tomber sous tes coups dans la vallée des Térébinthes, voici, est enveloppée dans une toile derrière l'Ephod; si tu veux la prendre prends-là; car ici il n'y en a pas d'autre que celle-là. Et David dit: Elle n'a pas sa pareille; donne-la moi.
Sai firist ya ce, “Takobin Goliyat Bafilistin nan wanda ka kashe a Kwarin Ela yana nan. An naɗe shi da ƙyallen aka ajiye a bayan Efod, in kana so, sai ka ɗauka. Ba wani takobi kuma sai wancan.” Dawuda ya ce, “Ba ni shi, ai, ba wani kamar sa.”
10 Et David se remit en route, continuant le jour même à fuir devant Saül, et il arriva chez Achis, Roi de Gath.
A ranar, Dawuda ya gudu daga wajen Shawulu ya tafi wuri Akish sarkin Gat.
11 Et les serviteurs d'Achis disaient de lui: N'est-ce pas David, le Roi du pays? N'est-ce pas à lui que dans les chœurs on chantait ces paroles: Saül a tué ses mille, et David ses dix mille!
Amma bayin Akish suka ce masa, “Wannan ba shi ne Dawuda sarkin ƙasar ba? Ashe, ba shi ne aka yi ta yin waƙoƙi a kansa, ana raye-raye, ana cewa, “Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?”
12 Et ces discours firent impression sur le cœur de David, qui prit une grande peur d'Achis, Roi de Gath.
Dawuda ya riƙe waɗannan kalmomi a zuciyarsa, ya kuma ji tsoron Akish sarkin Gat sosai.
13 Et il contrefit l'insensé devant eux, et il se démenait comme un furieux entre leurs mains, et il grattait les battants de la porte et laissait couler sa salive dans sa barbe.
Don haka sai ya yi kamar ya taɓu a gabansu. A duk lokacin da yake tare da su, sai yă yi kamar ya haukace. Ya yi ta zāne-zāne a ƙofofi, ya bar miyau yana ta bin gemunsa.
14 Alors Achis dit à ses serviteurs: Voici, vous voyez que cet homme est hors de sens; pourquoi me l'amenez-vous?
Akish ya ce wa bayinsa, “Duba, wannan mutum yana hauka. Me ya sa kuka kawo shi a wurina?
15 Manqué-je de fous, que vous m'amenez celui-ci pour m'exposer à ses accès? Doit-il entrer dans ma maison?
Na rasa masu hauka ne da za ku kawo mini wannan mutum yă yi ta hauka a gabana? Dole ne wannan mutum yă shiga gidana?”