< 1 Rois 11 >
1 Et le Roi Salomon aima des femmes étrangères en grand nombre, et d'abord la fille de Pharaon, puis des Moabites, des Ammonites, des iduméennes, des Sidoniennes, des Héthiennes,
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 appartenant aux peuples desquels l'Éternel avait dit aux enfants d'Israël: Vous n'entrerez point chez eux, et ils n'entreront point chez vous; certainement ils tourneront votre cœur du côté de leurs dieux; c'est à eux que Salomon s'attacha par l'amour.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 Et il avait en femmes sept cents princesses et trois cents concubines; et ses femmes firent dévier son cœur.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 Et à l'époque de la vieillesse de Salomon ses femmes tournèrent son cœur du côté d'autres dieux, et son cœur ne fut pas sans partage avec l'Éternel, son Dieu, comme le cœur de David, son père.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 Et Salomon se mit à la suite d'Astarté, divinité des Sidoniens, et de Milcom, l'Abominable des Ammonites.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 Et Salomon fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, et il ne s'attacha point complètement à l'Éternel comme David, son père.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Alors Salomon éleva un tertre à Camos, l'Abominable des Moabites, sur la montagne située devant Jérusalem, et à Moloch, l'Abominable des Ammonites.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 Et ainsi fit-il pour toutes ses femmes étrangères qui offraient de l'encens et des sacrifices à leurs dieux.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 Et l'Éternel se courrouça contre Salomon parce qu'il avait détourné son cœur de l'Éternel, Dieu d'Israël, qui lui était apparu deux fois,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 et lui avait donné sur ce point un ordre exprès en lui défendant de s'attacher à d'autres dieux; mais Salomon n'observa point la défense de l'Éternel.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 Et l'Éternel dit à Salomon: Puisque tu t'es ainsi comporté, et que tu n'as pas gardé mon alliance et mes statuts que je t'avais prescrits, je t'arracherai le royaume et le donnerai à ton serviteur;
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 cependant je ne le ferai pas de ton vivant, pour l'amour de David, ton père; c'est de la main de ton fils que je l'arracherai;
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 seulement ce n'est pas la totalité du royaume que je détacherai; je laisserai une Tribu à ton fils pour l'amour de David, mon serviteur, et pour l'amour de Jérusalem que j'ai choisie.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 Et l'Éternel suscita un adversaire à Salomon, Hadad, l'Iduméen, de la race royale qui régnait en Edom.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 Et il arriva, David étant en Idumée, lorsque Joab, général de l'armée, eut gagné les hauteurs pour donner la sépulture aux morts, que celui-ci massacra tous les mâles de l'Idumée
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (car Joab y resta six mois avec tous les Israélites jusqu'à ce qu'il eût exterminé tous les mâles de l'Idumée);
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 alors Hadad, ayant avec lui des Iduméens d'entre les serviteurs de son père, prit la fuite pour gagner l'Egypte; or Hadad était encore un jeune garçon.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 Et après être partis de Madian, ils atteignirent Pharan, et de Pharan ils emmenèrent du monde avec eux et ils arrivèrent en Egypte chez Pharaon, roi d'Egypte, lequel lui donna une demeure, et lui assigna des subsistances et lui concéda des terres.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 Et Hadad trouva à un haut degré grâce aux yeux de Pharaon, qui lui donna en mariage la sœur de sa femme, la sœur de la reine Thachpenès.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 Et la sœur de Thachpenès lui enfanta Genubath, son fils; et Thachpenès fit son sevrage au palais de Pharaon, et Genubath fut dans le palais de Pharaon au milieu des fils de Pharaon.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 Et Hadad ayant appris en Egypte que David reposait avec ses pères, et que Joab, général de l'armée, était mort, Hadad alors dit à Pharaon: Laisse-moi libre de retourner dans mon pays.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 Et Pharaon lui dit: Mais, que te manque-t-il chez moi? Et te voilà cherchant à aller dans ton pays! Et il reprit: Non, mais laisse, laisse-moi partir!
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 En outre Dieu suscita à Salomon un adversaire dans Rezon, fils d'Eljada, déserteur d'Hadadézer, roi de Tsoba, son maître.
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 Et il ramassa auprès de lui des hommes, et devint chef de bande, lorsque David en fit le carnage (des Syriens); et ils se portèrent à Damas, et ils s'y maintinrent, et dominèrent à Damas.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 Et il fut un adversaire pour Israël durant toute la vie de Salomon. Et quant au mal que fit Hadad, il harcela Israël et il régna sur la Syrie.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Et aussi Jéroboam, fils de Nebat, Ephraïmite de Tsérèda (or sa mère, veuve, s'appelait Tserua), sujet de Salomon, leva la main contre le Roi.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 Et voici la cause pour laquelle il leva la main contre le Roi: Salomon construisait la Redoute et fermait la brèche de la Cité de David, son père.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 Et le personnage, Jéroboam, était un brave, un homme de ressource, et Salomon voyant dans le jeune homme de l'aptitude à l'œuvre, le préposa sur tous les gens de charge de la maison de Joseph…
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 Et il arriva dans ce temps-là que Jéroboam, étant sorti de Jérusalem, fut rencontré par Ahia, de Silo, le prophète, dans la route; or Ahia portait un manteau neuf, et ils étaient seuls dans la campagne.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 Alors Ahia prit le manteau neuf qu'il avait sur lui et le déchira en douze morceaux
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 et dit à Jéroboam: Prends pour toi dix morceaux; car ainsi parle l'Éternel, Dieu d'Israël: Voici, je vais arracher le royaume de la main de Salomon, et te remettre les dix Tribus;
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 mais une Tribu lui restera en considération de mon serviteur David et en considération de Jérusalem, la ville que j'ai choisie dans la totalité des Tribus d'Israël,
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 parce que l'on m'a abandonné et que l'on a adoré Astarté, divinité des Sidoniens, Camos, dieu de Moab, et Milcom, dieu des Ammonites, et que l'on n'a pas pratiqué mes voies pour accomplir ce qui est droit à mes yeux, ni mes statuts, ni mes lois, comme David, son père.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Cependant je ne lui arracherai pas de la main la totalité du royaume, mais je lui laisserai sa place de Prince sa vie durant, en considération de David, mon serviteur, que j'ai choisi et qui a gardé mes commandements et mes statuts,
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 et j'arracherai le royaume de la main de son fils, et te donnerai les dix Tribus; quant à son fils,
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 je lui laisserai une Tribu, afin que mon serviteur David ait dans tous les temps une lampe devant moi à Jérusalem, la ville que je me suis choisie pour y placer mon Nom.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 Et je te prendrai pour que tu règnes sur tout ce qu'ambitionne ton âme et deviennes roi d'Israël.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 Et si tu obéis à tout ce que je te commanderai, et pratiques mes voies et fais ce qui est droit à mes yeux, gardant mes statuts et mes commandements, comme l'a fait David, mon serviteur, alors je serai avec toi et t'édifierai une maison stable, comme je l'ai édifiée à David, et je te donnerai Israël
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 et j'humilierai la race de David à cet effet, seulement pas pour toujours. —
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Et Salomon cherchait à se défaire de Jéroboam; alors Jéroboam partit, et s'enfuit en Egypte chez Sisac, roi d'Egypte, et il fut en Egypte jusqu'à la mort de Salomon.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 Et le reste de l'histoire de Salomon, et tous ses actes et sa sagesse sont consignés dans le livre de l'histoire de Salomon.
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 Et le temps que Salomon régna à Jérusalem sur tout Israël, fut quarante années.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 Et Salomon reposa à côté de ses pères et reçut la sépulture dans la ville de David, son père. Et Roboam, son fils, régna à sa place.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.