< Ruth 4 >

1 Booz monta donc à la porte de la ville, et s'y assit; et voici, celui qui avait le droit de rachat, dont Booz avait parlé, vint à passer; et Booz lui dit: Toi, un tel, détourne-toi, et assieds-toi ici. Et il se détourna, et s'assit.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Alors il prit dix hommes, d'entre les anciens de la ville, et il leur dit: Asseyez-vous ici; et ils s'assirent.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Puis il dit à celui qui avait le droit de rachat: Naomi, qui est revenue du pays de Moab, a vendu la portion d'un champ qui appartenait à Élimélec notre frère.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Et j'ai dit: Je veux t'en informer et te dire: Acquiers-la, en présence des habitants et des anciens de mon peuple; si tu veux la racheter, rachète-la; et si tu ne veux pas la racheter, déclare-le-moi, et que je le sache; car il n'y en a point d'autre avant toi qui ait le droit de rachat, et je l'ai après toi. Il répondit: Je rachèterai.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Alors Booz dit: Au jour que tu acquerras le champ, de la main de Naomi et de Ruth, la Moabite, femme du défunt, tu acquerras aussi Ruth, pour conserver le nom du défunt dans son héritage.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Et celui qui avait le droit de rachat dit: Je ne saurais racheter, de peur que je ne perde mon héritage; toi, prends pour toi mon droit de rachat; car je ne puis pas racheter.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 (Or, autrefois en Israël, en cas de rachat et de subrogation, pour confirmer la chose, l'homme ôtait son soulier et le donnait à son parent; cela servait de témoignage en Israël. )
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Celui qui avait le droit de rachat dit donc à Booz: Acquiers-le pour toi! et il ôta son soulier.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Alors Booz dit aux anciens et à tout le peuple: Vous êtes aujourd'hui témoins que j'ai acquis de la main de Naomi tout ce qui appartenait à Élimélec, et tout ce qui était à Kiljon et à Machlon;
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 Et que je me suis aussi acquis pour femme Ruth, la Moabite, femme de Machlon, pour conserver le nom du défunt dans son héritage, afin que le nom du défunt ne soit point retranché d'entre ses frères, et de la porte de sa ville; vous en êtes témoins aujourd'hui.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Et tout le peuple qui était à la porte, et les anciens, dirent: Nous en sommes témoins! L'Éternel rende la femme qui entre en ta maison, semblable à Rachel et à Léa, qui toutes deux ont bâti la maison d'Israël! Montre ta force en Éphrath, et fais-toi un nom dans Bethléhem!
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 Que la postérité que l'Éternel te donnera par cette jeune femme, rende ta maison semblable à la maison de Pharets, que Tamar enfanta à Juda!
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Ainsi Booz prit Ruth et elle fut sa femme; et il alla vers elle, et l'Éternel lui fit la grâce de concevoir, et elle enfanta un fils;
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Et les femmes dirent à Naomi: Béni soit l'Éternel, qui ne t'a pas laissée manquer aujourd'hui d'un homme qui eût droit de rachat; puisse son nom être conservé en Israël!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 Qu'il console ton âme, et qu'il soit le soutien de ta vieillesse; car ta belle-fille, qui t'aime, a enfanté, et elle te vaut mieux que sept fils.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 Alors Naomi prit l'enfant, et le mit dans son sein, et elle lui tenait lieu de nourrice.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 Et les voisines lui donnèrent un nom, et dirent: Un fils est né à Naomi; et elles l'appelèrent Obed; ce fut le père d'Isaï, père de David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 Or, ce sont ici les générations de Pharets: Pharets fut père de Hetsron;
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 Hetsron fut père de Ram; Ram fut père d'Amminadab;
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 Amminadab fut père de Nahasshon; Nahasshon fut père de Salmon;
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 Salmon fut père de Booz; Booz fut père d'Obed;
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 Obed fut père d'Isaï, et Isaï fut père de David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >