< Ruth 1 >
1 Il arriva, aux jours du gouvernement des juges, qu'il y eut une famine dans le pays, et un homme de Bethléhem de Juda s'en alla habiter la campagne de Moab, lui, sa femme, et ses deux fils.
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2 Le nom de cet homme était Élimélec, et le nom de sa femme Naomi, et les noms de ses deux fils Machlon et Kiljon; ils étaient Éphratiens, de Bethléhem de Juda, et ils vinrent dans la campagne de Moab, et ils s'y établirent.
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3 Or, Élimélec, mari de Naomi, mourut, et elle resta avec ses deux fils.
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
4 Ceux-ci épousèrent des femmes moabites, dont l'une s'appelait Orpa, et l'autre Ruth; et ils demeurèrent là environ dix ans.
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5 Puis, Machlon et Kiljon étant morts aussi, cette femme demeura seule, privée de ses deux fils et de son mari.
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
6 Alors elle se leva avec ses belles-filles, pour s'en retourner de la campagne de Moab; car elle y avait appris que l'Éternel avait visité son peuple, en lui donnant du pain.
Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
7 Elle sortit donc du lieu où elle avait demeuré, et ses deux belles-filles avec elle; et elles se mirent en chemin pour retourner au pays de Juda.
Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
8 Et Naomi dit à ses deux belles-filles: Allez, retournez chacune à la maison de sa mère. L'Éternel vous traite avec bonté, comme vous avez fait à ceux qui sont morts, et à moi!
Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
9 L'Éternel vous fasse trouver du repos à chacune dans la maison d'un mari! Et elle les baisa. Mais elles élevèrent la voix et pleurèrent,
Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
10 Et lui dirent: Nous retournerons avec toi vers ton peuple.
suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
11 Mais Naomi répondit: Retournez, mes filles; pourquoi viendriez-vous avec moi? Ai-je encore dans mon sein des fils qui puissent devenir vos maris?
Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
12 Retournez, mes filles, allez. Je suis trop âgée pour me remarier; et quand je dirais: J'ai de l'espérance; et quand cette nuit même je serais avec un mari, et que j'enfanterais des fils,
Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
13 Attendriez-vous jusqu'à ce qu'ils devinssent grands? Resteriez-vous confinées sans vous remarier? Non, mes filles; car je suis en plus grande amertume que vous, parce que la main de l'Éternel s'est appesantie sur moi.
za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
14 Alors elles élevèrent leur voix et pleurèrent encore. Et Orpa baisa sa belle-mère; mais Ruth s'attacha à elle.
A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
15 Alors Naomi dit: Voici, ta belle-sœur s'en est allée vers son peuple et vers ses dieux; retourne après ta belle-sœur.
Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
16 Mais Ruth répondit: Ne me presse pas de te laisser, pour m'éloigner de toi; car où tu iras j'irai, et où tu demeureras je demeurerai; ton peuple sera mon peuple, et ton Dieu sera mon Dieu;
Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
17 Où tu mourras je mourrai, et j'y serai ensevelie. Que l'Éternel me traite avec la dernière rigueur, si autre chose que la mort me sépare de toi!
Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
18 Naomi, voyant donc qu'elle était résolue d'aller avec elle, cessa de lui en parler.
Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
19 Et elles marchèrent toutes deux jusqu'à ce qu'elles arrivassent à Bethléhem. Et comme elles entraient dans Bethléhem, toute la ville fut émue à cause d'elles, et les femmes disaient: N'est-ce pas Naomi?
Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
20 Et elle leur répondit: Ne m'appelez point Naomi (la belle), appelez-moi Mara (amère); car le Tout-Puissant m'a remplie d'amertume.
Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
21 Je suis partie dans l'abondance, et l'Éternel me ramène vide. Pourquoi m'appelleriez-vous Naomi, puisque l'Éternel m'a abattue, et que le Tout-Puissant m'a affligée?
In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
22 C'est ainsi que Naomi s'en retourna avec Ruth, la Moabite, sa belle-fille, qui était venue de la campagne de Moab. Et elles entrèrent dans Bethléhem, au commencement de la moisson des orges.
Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.