< Psaumes 89 >
1 Je chanterai à jamais les bontés de l'Éternel; ma bouche publiera ta fidélité d'âge en âge.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Car j'ai dit: Ta bonté subsiste à jamais; tu établis ta fidélité dans les cieux.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 J'ai traité alliance avec mon élu; j'ai fait serment à David, mon serviteur, disant:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 J'affermirai ta postérité pour toujours, et je fonderai ton trône pour tous les âges. (Sélah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Les cieux, ô Éternel, célèbrent tes merveilles et ta fidélité dans l'assemblée des saints.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Car qui, dans les lieux célestes, est comparable à l'Éternel? qui ressemble à l'Éternel parmi les fils des dieux?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Dieu est terrible dans l'assemblée des saints, redoutable plus que tous ceux qui l'environnent.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Éternel, Dieu des armées, qui est puissant comme toi, ô Éternel? Tu es environné de ta fidélité.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu domines sur l'orgueil de la mer; quand ses vagues s'élèvent, toi, tu les apaises.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu as abattu Rahab comme un blessé à mort; par ton bras puissant tu as dissipé tes ennemis.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 A toi sont les cieux, à toi aussi la terre; tu as fondé le monde et ce qu'il renferme.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Tu as créé le nord et le midi; le Thabor et l'Hermon poussent des cris de joie à ton nom.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Ton bras est puissant, ta main forte, ta droite élevée.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 La justice et l'équité sont la base de ton trône; la grâce et la vérité marchent devant ta face.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Heureux le peuple qui connaît les cris de joie! Éternel, ils marchent à la clarté de ta face.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Ils se réjouissent en ton nom chaque jour, et se glorifient de ta justice.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Car tu es leur gloire et leur force; c'est par ta faveur que notre corne est élevée.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Car l'Éternel est notre bouclier; le Saint d'Israël est notre roi.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Tu parlas jadis à ton bien-aimé dans une vision, et tu dis: J'ai prêté secours à un homme fort; j'ai élevé du milieu du peuple un héros;
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 J'ai trouvé David mon serviteur, je l'ai oint de mon huile sainte;
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Ma main sera constamment avec lui, et mon bras le fortifiera;
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 L'ennemi ne pourra le surprendre, et l'homme inique ne l'opprimera point;
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Je briserai devant lui ses adversaires, et je frapperai ceux qui le haïssent;
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Ma fidélité, ma faveur seront avec lui, et sa force s'élèvera par mon nom;
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Je mettrai sa main sur la mer, et sa droite sur les fleuves.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Il m'invoquera, disant: Tu es mon Père, mon Dieu et le rocher de mon salut.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Aussi j'en ferai le premier-né, le souverain des rois de la terre.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Je lui conserverai ma faveur à toujours, et mon alliance lui est assurée.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Je rendrai sa postérité éternelle, et son trône comme les jours des cieux.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Si ses fils abandonnent ma loi, et ne marchent pas selon mes ordonnances;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 S'ils violent mes statuts, et ne gardent pas mes commandements;
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Je châtierai leur transgression par la verge, et leur iniquité par des plaies.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Mais je ne lui retirerai pas ma bonté, et ne lui fausserai point ma foi.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Je ne violerai point mon alliance, et ne changerai pas ce qui est sorti de mes lèvres.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 J'ai une fois juré par ma sainteté; je ne mentirai point à David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Sa postérité subsistera toujours, et son trône aussi longtemps que le soleil devant moi.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Comme la lune, il durera à jamais; et il y en a dans les cieux un témoin fidèle.
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Cependant tu l'as rejeté, tu l'as méprisé; tu t'es indigné contre ton Oint;
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Tu as repoussé l'alliance de ton serviteur; tu as jeté à terre et profané sa couronne.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Tu as rompu toutes ses barrières; tu as ruiné ses forteresses.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Tous ceux qui passent au chemin le pillent; il est en opprobre à ses voisins.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Tu as élevé la droite de ses adversaires, tu as réjoui tous ses ennemis;
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Tu as fait plier la pointe de son épée et ne l'as pas soutenu dans le combat.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Tu as fait cesser son éclat, et tu as jeté son trône à terre;
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Tu as abrégé les jours de sa jeunesse, et tu l'as couvert de honte. (Sélah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Jusques à quand, Éternel, te cacheras-tu sans cesse, et ta colère sera-t-elle embrasée comme un feu?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Rappelle-toi quelle est ma durée, pour quel néant tu as créé tous les fils des hommes.
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Quel homme pourra vivre et ne point voir la mort? Qui sauvera son âme de la main du Sépulcre? (Sélah) (Sheol )
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol )
49 Seigneur, où sont tes bontés premières, que tu juras à David sur ta fidélité?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Souviens-toi, Seigneur, de l'opprobre de tes serviteurs; et que je porte en mon sein l'opprobre fait par tous ces grands peuples.
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Car tes ennemis ont outragé, ô Éternel, tes ennemis ont outragé les pas de ton Oint.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Béni soit l'Éternel à toujours! Amen, oui, amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!