< Psaumes 66 >

1
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Chantez la gloire de son nom; louez-le, et lui rendez gloire!
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dites à Dieu: Que tes œuvres sont redoutables! A cause de la grandeur de ta force, tes ennemis viendront se soumettre à toi.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toute la terre se prosternera devant toi; elle chantera en ton honneur, elle chantera ton nom. (Sélah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venez, et voyez les œuvres de Dieu; il est redoutable dans ce qu'il fait envers les fils des hommes.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Il a changé la mer en terre sèche; on passait à pied dans le fleuve; là nous nous sommes réjouis en lui.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Il domine éternellement par sa puissance; ses yeux observent les nations, pour que les rebelles ne s'élèvent pas. (Sélah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Peuples, bénissez notre Dieu, et faites entendre la voix de sa louange!
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Lui qui a conservé la vie à notre âme, et qui n'a pas permis que nos pieds bronchassent.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Car tu nous as éprouvés, ô Dieu; tu nous as fait passer au creuset comme l'argent.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tu nous avais amenés dans le filet; tu avais mis sur nos reins un pesant fardeau;
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Tu avais fait monter les hommes sur nos têtes; nous étions entrés dans le feu et dans l'eau; mais tu nous as mis au large et dans l'abondance.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 J'entrerai dans ta maison avec des holocaustes; et je te rendrai mes vœux,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Que mes lèvres ont proférés et que ma bouche a prononcés dans ma détresse.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Je t'offrirai des brebis grasses en holocauste, avec les béliers fumant sur l'autel; je sacrifierai des taureaux avec des boucs. (Sélah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Vous tous qui craignez Dieu, venez, écoutez, et je raconterai ce qu'il a fait à mon âme.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Je l'ai invoqué de ma bouche; aussi ma langue l'exaltera.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si j'eusse pensé quelque iniquité dans mon cœur, le Seigneur ne m'eût point écouté.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Mais certainement Dieu m'a écouté; il a prêté l'oreille à la voix de ma prière.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Béni soit Dieu qui n'a point rejeté ma prière, ni retiré de moi sa bonté!
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psaumes 66 >