< Psaumes 60 >

1 Lorsqu'il fit la guerre avec les Syriens de Mésopotamie et avec les Syriens de Tsoba, et que Joab revint et défit douze mille Édomites dans la vallée du Sel. O Dieu, tu nous as rejetés, tu nous as dispersés, tu t'es irrité; rétablis-nous!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Tu as fait trembler la terre, tu l'as déchirée; répare ses brèches, car elle est ébranlée.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Tu as fait voir à ton peuple des choses dures; tu nous as abreuvés d'un vin d'étourdissement.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 Mais tu as donné à ceux qui te craignent un étendard
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 Afin que tes bien-aimés soient délivrés; sauve-nous par ta droite, et nous exauce!
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 Dieu a parlé dans son sanctuaire; je me réjouirai; je partagerai Sichem, et je mesurerai la vallée de Succoth:
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Galaad est à moi; à moi Manassé; Éphraïm est le rempart de ma tête; Juda mon législateur;
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab est le bassin où je me lave; je jette mon soulier sur Édom; terre des Philistins, pousse des acclamations à mon honneur!
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Qui me conduira vers la ville forte? Qui me mènera jusqu'en Édom?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 N'est-ce pas toi, ô Dieu, qui nous avais rejetés, qui ne sortais plus, ô Dieu, avec nos armées?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Donne-nous du secours pour sortir de détresse; car
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 En Dieu nous combattrons avec vaillance, et c'est lui qui foulera nos adversaires.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.

< Psaumes 60 >