< Psaumes 6 >

1 Éternel, ne me reprends pas dans ton indignation, et ne me châtie pas dans ta colère.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Bisa ga sheminit. Ta Dawuda. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 Aie pitié de moi, Éternel! car je suis sans force; Éternel, guéris-moi, car mes os sont tremblants.
Ka yi mini jinƙai, Ubangiji, gama na suma; Ya Ubangiji, ka warkar da ni, gama ƙasusuwana suna zafin ciwo.
3 Mon âme aussi est fort troublée; et toi, Éternel, jusques à quand?
Raina yana cikin wahala. Har yaushe, ya Ubangiji, har yaushe?
4 Reviens, Éternel, délivre mon âme; sauve-moi pour l'amour de ta bonté!
Ka juyo, ya Ubangiji, ka cece ni; ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka.
5 Car dans la mort on ne se souvient point de toi; qui te célébrera dans le Sépulcre? (Sheol h7585)
Babu wanda yakan tuna da kai sa’ad da ya mutu. Wa ke yabonka daga kabari? (Sheol h7585)
6 Je m'épuise à gémir; chaque nuit je baigne ma couche de pleurs, je trempe mon lit de mes larmes.
Na gaji tiƙis daga nishi. Dukan dare na jiƙe gadona da kuka na jiƙe kujerata da hawaye.
7 Mon visage est tout défait de chagrin; il dépérit à cause de tous mes ennemis.
Idanuna sun rasa ƙarfi da baƙin ciki; sun rasa ƙarfi saboda dukan abokan gābana.
8 Éloignez-vous de moi, vous tous, ouvriers d'iniquité! Car l'Éternel a entendu la voix de mes pleurs.
Ku tafi daga gare ni, dukanku masu aikata mugunta, gama Ubangiji ya ji kukata.
9 L'Éternel a entendu ma supplication, l'Éternel reçoit ma prière.
Ubangiji ya ji kukata saboda jinƙansa; Ubangiji ya karɓi addu’ata.
10 Tous mes ennemis seront confus et saisis d'effroi; ils reculeront, ils seront soudain couverts de honte.
Dukan abokan gābana za su sha kunya su kuma karaya; za su juya da kunya nan da nan.

< Psaumes 6 >