< Psaumes 56 >
1 O Dieu, aie pitié de moi, car les hommes me poursuivent; tout le jour ils me font la guerre, ils me pressent.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Tout le jour mes adversaires me poursuivent; car plusieurs font la guerre contre moi, ô Dieu Très-Haut!
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 Le jour où je craindrai, je me confierai en toi.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 Je louerai Dieu et sa promesse; je me confie en Dieu, je ne crains rien; que me ferait l'homme?
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 Tout le jour ils tordent mes paroles; ils ne pensent qu'à me nuire.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 Ils s'assemblent; ils se tiennent cachés; ils observent mes pas, car ils en veulent à ma vie.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 Ils comptent sur l'iniquité pour se sauver. O Dieu, précipite les peuples dans ta colère!
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 Tu comptes mes allées et mes venues; mets mes larmes dans tes vaisseaux; ne sont-elles pas dans ton livre?
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 Le jour où je crierai à toi, mes ennemis seront repoussés en arrière; je sais que Dieu est pour moi.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 Je louerai Dieu et sa promesse; je louerai l'Éternel et sa promesse.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 Je m'assure en Dieu; je ne crains rien; que me ferait l'homme?
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 O Dieu, j'accomplirai les vœux que je t'ai faits; je te rendrai des actions de grâces.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 Car tu as délivré mon âme de la mort et mes pieds de chute, afin que je marche devant Dieu, dans la lumière des vivants.
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.