< Psaumes 27 >

1 Psaume de David. L'Éternel est ma lumière et ma délivrance; de qui aurais-je peur? L'Éternel est le rempart de ma vie; de qui aurais-je de la crainte?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 Quand les méchants, mes adversaires et mes ennemis, sont venus contre moi pour me dévorer, eux-mêmes ont bronché et sont tombés.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Quand une armée camperait contre moi, mon cœur ne craindrait point; quand la guerre s'élèverait contre moi, ce sera là ma confiance.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 J'ai demandé une seule chose à l'Éternel, et je la rechercherai: c'est d'habiter dans la maison de l'Éternel tous les jours de ma vie, pour contempler la beauté de l'Éternel, et pour visiter son palais.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 Car il m'abritera dans sa tente au mauvais jour; il me cachera dans le lieu secret de son tabernacle; il m'élèvera comme sur un rocher.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 Et maintenant ma tête s'élèvera au-dessus de mes ennemis qui sont autour de moi; j'offrirai dans son tabernacle des sacrifices de cris de joie; je chanterai et je psalmodierai à l'Éternel.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Éternel, écoute ma voix, je t'invoque; aie pitié de moi et m'exauce!
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 Mon cœur me dit de ta part: Cherchez ma face. Je cherche ta face, ô Éternel!
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Ne me cache pas ta face! Ne rejette pas ton serviteur dans ton courroux! Tu as été mon aide; ne me délaisse pas, ne m'abandonne pas, Dieu de mon salut!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 Quand mon père et ma mère m'auraient abandonné, l'Éternel me recueillera.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Éternel, enseigne-moi ta voie, et me conduis dans le droit chemin, à cause de mes ennemis.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Ne me livre pas au désir de mes adversaires; car de faux témoins et qui ne respirent que violence, se sont élevés contre moi.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 Ah! si je n'avais cru que je verrais les biens de l'Éternel dans la terre des vivants!
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Attends-toi à l'Éternel, demeure ferme, que ton cœur se fortifie; oui, attends-toi à l'Éternel!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.

< Psaumes 27 >