< Psaumes 25 >

1 Psaume de David. Éternel, j'élève mon âme à toi.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 Mon Dieu, je m'assure en toi; que je ne sois pas rendu confus, que mes ennemis ne se réjouissent pas à mon sujet
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Certes, aucun de ceux qui s'attendent à toi, ne sera confus; ceux-là seront confus, qui agissent avec perfidie, sans cause.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Éternel, fais-moi connaître tes voies, enseigne-moi tes sentiers!
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Fais-moi marcher dans ta vérité et m'enseigne; car tu es le Dieu de ma délivrance, je m'attends à toi tout le jour.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Souviens-toi de tes compassions, ô Éternel, et de tes bontés; car elles sont de tout temps.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Ne te souviens point des péchés de ma jeunesse, ni de mes transgressions; selon ta miséricorde, souviens-toi de moi, à cause de ta bonté, ô Éternel!
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 L'Éternel est bon et droit; c'est pourquoi il enseignera aux pécheurs le chemin qu'ils doivent suivre.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Il fera marcher les humbles dans la justice; il enseignera sa voie aux humbles.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Tous les sentiers de l'Éternel ne sont que bonté et fidélité, pour ceux qui gardent son alliance et ses témoignages.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 Pour l'amour de ton nom, ô Éternel, tu me pardonneras mon iniquité; car elle est grande.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Quel est l'homme qui craint l'Éternel? Il lui enseignera le chemin qu'il doit choisir.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 Son âme habitera parmi les biens, et sa postérité possédera la terre.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 Le secret de l'Éternel est pour ceux qui le craignent, et il leur fera connaître son alliance.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mes yeux regardent sans cesse vers l'Éternel; car il fera sortir mes pieds du filet.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Tourne-toi vers moi, et prends pitié de moi, car je suis seul et affligé!
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Les détresses de mon cœur se sont augmentées; délivre-moi de mes angoisses!
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Vois mon affliction et mon travail, et me pardonne tous mes péchés!
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Vois mes ennemis, car ils sont nombreux, et ils me haïssent d'une haine violente.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Garde mon âme, et me délivre; que je ne sois pas confus, car je me suis retiré vers toi!
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Que l'intégrité et la droiture me préservent, car je me suis attendu à toi!
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 O Dieu! rachète Israël de toutes ses détresses.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Psaumes 25 >