< Psaumes 21 >
1 Éternel, le roi se réjouit de ta puissance, et quelle allégresse lui donne ton salut!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ya Ubangiji, sarki yana farin ciki cikin ƙarfinka. Yana farin cikinsa ƙwarai cikin nasarorin da ka ba shi!
2 Tu lui as accordé le désir de son cœur, et ne lui as pas refusé la prière de ses lèvres. (Sélah)
Ka biya masa bukatar zuciyarsa ba ka kuwa hana masa roƙon da ya yi da leɓunansa ba. (Sela)
3 Car tu l'as prévenu par des bénédictions excellentes; tu as mis sur sa tête une couronne d'or fin.
Ka marabce shi da yalwar albarka ka kuma sa masa rawanin zallan zinariya a kansa.
4 Il te demandait la vie; tu la lui as donnée, une longue durée de jours, à perpétuité, à jamais.
Ya nemi ka ba shi rai, ka kuwa ba shi, tsawo kwanaki, har abada abadin
5 Sa gloire est grande par ta délivrance; tu le revêts de splendeur et de majesté.
Ta wurin nasarorin da ka ba shi, ɗaukakarsa mai girma ce; ka mayar masa ɗaukaka da kuma suna.
6 Car tu fais de lui l'objet de tes bénédictions pour toujours, tu le combles de joie en ta présence.
Tabbatacce ka ba shi madawwamiyar albarka ka kuma sa shi murna da farin cikin kasancewarka.
7 Le roi met sa confiance en l'Éternel, et par la bonté du Très-Haut, il ne sera point ébranlé.
Gama sarki ya dogara gare ka Ubangiji ta wurin ƙauna marar ƙarewa ta Mafi Ɗaukaka ba zai jijjigu ba.
8 Ta main atteindra tous tes ennemis, ta droite atteindra ceux qui te haïssent.
Hannunka zai kakkama dukan abokan gābanka; hannunka na dama zai kakkama masu ƙinka.
9 Tu les rendras tels qu'un four ardent, quand tu paraîtras; l'Éternel les engloutira dans sa colère, et le feu les consumera.
A lokacin bayyanarka za ka sa su zama kamar wutar matoya. Cikin fushinsa Ubangiji zai haɗiye su, kuma wutarsa za tă cinye su.
10 Tu feras périr leur fruit de dessus la terre, et leur race d'entre les fils des hommes.
Za ka hallaka’ya’yansu daga duniya, zuriyarsu kuma daga’yan adam.
11 Car ils ont projeté du mal contre toi; ils ont formé des desseins qu'ils ne pourront exécuter.
Ko da yake suna shirya maka mugunta suna kuma ƙirƙiro mugayen dabaru, ba za su yi nasara ba;
12 Car tu les mettras en fuite, tu armeras ton arc contre leur face.
gama za ka sa su juye bayansu sa’ad da ka auna su da bakan da ka ja.
13 Élève-toi, ô Éternel, dans ta force! Nous chanterons et nous célébrerons ta puissance!
Ka sami ɗaukaka, ya Ubangiji cikin ƙarfinka; za mu rera mu kuma yabi ikonka.