< Psaumes 135 >
1 Louez l'Éternel! Louez le nom de l'Éternel; louez-le, serviteurs de l'Éternel!
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Vous qui vous tenez dans la maison de l'Éternel, dans les parvis de la maison de notre Dieu,
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Louez l'Éternel, car l'Éternel est bon! Chantez à son nom, car il est clément!
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Car l'Éternel s'est choisi Jacob et Israël pour sa possession.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Car je sais que l'Éternel est grand, et notre Seigneur au-dessus de tous les dieux.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 L'Éternel fait tout ce qui lui plaît dans les cieux et sur la terre, dans les mers et dans tous les abîmes.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 C'est lui qui fait monter du bout de la terre les vapeurs; qui produit les éclairs et la pluie; qui tire le vent de ses trésors.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 C'est lui qui a frappé les premiers-nés d'Égypte, depuis les hommes jusqu'aux bêtes;
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 Qui a envoyé des signes et des prodiges au milieu de toi, Égypte, contre Pharaon et contre tous ses serviteurs;
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Qui a frappé plusieurs nations, et mis à mort de puissants rois:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon, roi des Amoréens, et Og, roi de Bassan, et tous les rois de Canaan;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 Et qui a donné leur pays en héritage, en héritage à Israël, son peuple.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Éternel, ton nom subsiste à toujours; Éternel, ta mémoire est d'âge en âge.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Car l'Éternel fera justice à son peuple, et il aura compassion de ses serviteurs.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Les idoles des nations sont de l'argent et de l'or, un ouvrage de mains d'homme.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Elles ont une bouche, et ne parlent point; elles ont des yeux, et ne voient point;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Elles ont des oreilles, et n'entendent point; il n'y a pas non plus de souffle dans leur bouche.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Ceux qui les font et tous ceux qui s'y confient leur deviendront semblables!
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Maison d'Israël, bénissez l'Éternel! Maison d'Aaron, bénissez l'Éternel!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Maison de Lévi, bénissez l'Éternel! Vous qui craignez l'Éternel, bénissez l'Éternel!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Béni soit, de Sion, l'Éternel qui réside à Jérusalem! Louez l'Éternel!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.